Labarai
Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa
Usman Muhammad Zaria
Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa wato (National Health Fellows) a Jihar Jigawa.
Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala aikin, Mataimakin Darakta kuma Mai Taimaka wa Darakta-Janar na Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa, Dakta Jibrin Muhammad Bashar, ya bayyana cewa aikin daukar ma’aikatan wani shiri ne na Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya karkashin jagorancin Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate.

Dakta Bashar, wanda kuma shi ne Babban Mai Kula da aikin daukar ma’aikatan a Jihar Jigawa, ya bayyana cewa shirin na da nufin zaben Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa da za su rika sa ido kan aiwatar da Asusun Kula da Lafiya na Asali (Basic Health Care Provision Fund) a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar.

A cewarsa, wadannan ma’aikata za su kasance jakadu na Asusun Kula da Lafiya na Gwamnatin Tarayya, wanda Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Kasa (National Primary Health Care Development Agency) ke kula da shi.

Ya kara da cewa an kirkiri asusun ne domin tallafa wa rukunin al’umma masu rauni, ciki har da mata, yara da tsofaffi, ta hanyar samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya da kuma tallafin kudi.

Ya bayyana cewa za a zabi mutum ashirin da bakwai, inda kowane daya zai wakilci daya daga cikin kananan hukumomi ashirin da bakwai na Jihar Jigawa.
Dakta Bashar ya nuna gamsuwa da yadda aka gudanar da aikin daukar ma’aikatan, inda ya yaba wa kwamitin daukar ma’aikata na jihar da kwamitin bisa kwarewa, gaskiya da kuma rashin nuna bangaranci yayin aikin.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai13 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
