Connect with us

Labarai

Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Published

on

Usman Muhammad Zaria 

Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa wato (National Health Fellows) a Jihar Jigawa.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala aikin, Mataimakin Darakta kuma Mai Taimaka wa Darakta-Janar na Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa, Dakta Jibrin Muhammad Bashar, ya bayyana cewa aikin daukar ma’aikatan wani shiri ne na Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya karkashin jagorancin Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate.

Dakta Bashar, wanda kuma shi ne Babban Mai Kula da aikin daukar ma’aikatan a Jihar Jigawa, ya bayyana cewa shirin na da nufin zaben Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa da za su rika sa ido kan aiwatar da Asusun Kula da Lafiya na Asali (Basic Health Care Provision Fund) a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar.

A cewarsa, wadannan ma’aikata za su kasance jakadu na Asusun Kula da Lafiya na Gwamnatin Tarayya, wanda Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Kasa (National Primary Health Care Development Agency) ke kula da shi.

Ya kara da cewa an kirkiri asusun ne domin tallafa wa rukunin al’umma masu rauni, ciki har da mata, yara da tsofaffi, ta hanyar samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya da kuma tallafin kudi.

Ya bayyana cewa za a zabi mutum ashirin da bakwai, inda kowane daya zai wakilci daya daga cikin kananan hukumomi ashirin da bakwai na Jihar Jigawa.

Dakta Bashar ya nuna gamsuwa da yadda aka gudanar da aikin daukar ma’aikatan, inda ya yaba wa kwamitin daukar ma’aikata na jihar da kwamitin  bisa kwarewa, gaskiya da kuma rashin nuna bangaranci yayin aikin.

Labarai

Labarai13 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara