Labarai
NEMA Ta Bada Tallafi Ga Wadanda Gobara Ta Shafa A Kauran Namoda
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta gabatar da kayan agaji ga gwamnatin jihar Zamfara domin tallafawa wadanda gobara ta shafa a wata makarantar Islamiyya da ke Kaura Namoda.
A lokacin da take mika kayayyakin, Darakta Janar na Hukumar Hajia Zubaida Umar, ta ce matakin ya nuna damuwar gwamnatin tarayya kan halin da wadanda abin ya shafa ke ciki.

Babbar Daraktar wanda shugaban NEMA shiyar Sokoto, Aliyu Shehu Kafindangi ya wakilta, ya ce tallafin ya hada da kayan abinci kamar buhunan shinkafa, da masara, da man girki, da kayayyakin amfani gida.
A baya dai Hajiya Zubaida Umar ta ziyarci wadanda lamarin ya rutsa da su wadanda har yanzu suke ci gaba da karbar magani a asibitin mata da yara na Khadijah da ke Kaura Namoda.

A asibitin, wakilin na shugabar ta NEMA, ya kuma gabatar da kayayyakin jinya ga hukumar lafiya matakin farko domin ci gaba da kula da wadanda abin ya shafa.
Ya kuma jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki da suka hada da wakilan hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Zamfara ZEMA, da ma’aikatar jin kai ta jihar Zamfara, da kuma karamar hukumar Kaura Namoda zuwa wurin da lamarin ya faru domin jajanta wa makarantar.

Wadanda suka karbi kayayyakin da hukumar ta NEMA ta bayar, a madadin gwamnatin jihar sun hada da babban sakatariyar hukumar ta ZEMA, wadda Daraktan Yaki da iftila’i, Hassan Usman Dauran, da wakilta, da Sarkin Kaura-namoda, Alhaji Sanusi Muhammad Asha da kuma kwamishinan ma’aikatar jin kai ta jihar Zamfara, wanda babban sakataren ma’aikatar Mohammed Bashir Maradun ya wakilta.
Haka kuma tawagar ta kai ziyarar ban girma ga Sarkin Kaura-namoda, Alhaji Sanusi Muhammad Asha a fadarsa.

Tun da farko, Sarkin Kauran Namoda, Alhaji Sanusi Asha, ya yi alkawarin sanya ido kan rabon kayan abincin ga wadanda abin ya shafa da kwamitin bayar da agajin gaggawa da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi suka kafa.
Hakazalika, ZEMA da ma’aikatar jin kai ta jihar, sun yabawa hukumar NEMA bisa wannan karimcin.
Daga Aminu Dalhatu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
