Connect with us

Labarai

NEMA Ta Bada Tallafi Ga Wadanda Gobara Ta Shafa A Kauran Namoda

Published

on

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA ta gabatar da kayan agaji ga gwamnatin jihar Zamfara domin tallafawa wadanda gobara ta shafa a wata makarantar Islamiyya da ke Kaura Namoda.

 

A lokacin da take mika  kayayyakin, Darakta Janar na Hukumar Hajia Zubaida Umar, ta ce matakin ya nuna damuwar gwamnatin tarayya kan halin da wadanda abin ya shafa ke ciki.

Babbar Daraktar wanda shugaban NEMA shiyar Sokoto, Aliyu Shehu Kafindangi ya wakilta, ya ce tallafin ya hada da kayan abinci kamar buhunan shinkafa, da masara, da man girki, da kayayyakin amfani  gida.

A baya dai Hajiya Zubaida Umar ta ziyarci wadanda lamarin ya rutsa da su wadanda har yanzu suke ci gaba da karbar magani a asibitin mata da yara na Khadijah da ke Kaura Namoda.

A asibitin, wakilin na shugabar ta NEMA, ya kuma gabatar da kayayyakin jinya ga hukumar lafiya matakin farko domin ci gaba da kula da wadanda abin ya shafa.

Ya kuma jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki da suka hada da wakilan hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Zamfara ZEMA, da  ma’aikatar jin kai ta jihar Zamfara, da kuma karamar hukumar Kaura Namoda zuwa wurin da lamarin ya faru domin jajanta wa makarantar.

Wadanda suka karbi kayayyakin da hukumar ta NEMA ta bayar, a madadin gwamnatin jihar sun hada da babban sakatariyar hukumar ta ZEMA, wadda Daraktan Yaki da iftila’i, Hassan Usman Dauran, da wakilta, da Sarkin Kaura-namoda, Alhaji Sanusi Muhammad Asha da kuma kwamishinan ma’aikatar jin kai ta jihar Zamfara, wanda babban sakataren ma’aikatar  Mohammed Bashir Maradun ya wakilta.

Haka kuma tawagar ta kai ziyarar ban girma ga Sarkin Kaura-namoda, Alhaji Sanusi Muhammad Asha a fadarsa.

Tun da farko, Sarkin Kauran Namoda, Alhaji Sanusi Asha, ya yi alkawarin sanya ido kan rabon kayan abincin ga wadanda abin ya shafa da kwamitin bayar da agajin gaggawa da gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi suka kafa.

Hakazalika, ZEMA da ma’aikatar jin kai ta jihar, sun yabawa hukumar NEMA bisa wannan karimcin.

Daga Aminu Dalhatu

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara