Labarai
NDLEA Kano Ta Kama Mutane 1,389 a 2025
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), reshen Kano, ta samu gagarumar nasara a shekarar 2025, inda ta kama mutane 1,389 da ake zargi da laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi, tare da kwace kilogiram 7,773.06 na nau’o’in miyagun ƙwayoyi daban-daban, ciki har da tabar wiwi, da ta aljannu da kokin da a farci kasa da kuma ƙwayoyin maye na kwakwalwa.
Wadannan alkaluma, kamar yadda Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad Maigatari, ya bayyana, sun nuna irin gagarumar nasarar da rundunar ta samu ƙarƙashin jagorancin Kwamanda CN D.Y. Lawal wajen yaƙi da fatauci da shan miyagun ƙwayoyi a faɗin jihar Kano.
Daga cikin waɗanda aka kama, 1,346 maza ne yayin da mata 43 ne. Haka kuma rundunar ta samu hukunci 141 a kotu, lamarin da ya zama darasi ga masu shirin aikata irin waɗannan laifuka, inda manyan dillalan miyagun ƙwayoyi guda huɗu suka samu hukuncin da ya kai shekaru 33 a gidan yari gaba ɗaya.
Baya ga kamen mutane da gurfanarwa, rundunar ta kuma samu nasarar kwace wani gida da aka mallaka ta hanyar kudaden miyagun ƙwayoyi, tare da kwace wasu kadarori biyu na wucin gadi, yayin da shari’o’i 133 ke ci gaba da sauraro a Kotun Tarayya.
A fannin gyara da wayar da kan jama’a, NDLEA Kano ta ba da muhimmanci ga shirin farfaɗo da masu shaye-shaye da hulɗa da al’umma. Mutane 94 sun kammala shirye-shiryen gyaran hali na musamman, yayin da mutane 1,009 (ciki har da mata 28) suka samu shawarwari na gajeren lokaci.
Rundunar ta gudanar da kamfe 254 na yaƙi da miyagun ƙwayoyi a makarantu, kasuwanni da cibiyoyin al’umma, inda ta kai saƙon wayar da kai ga mutane 86,939 (maza 41,225 da mata 45,714) ta hanyar taruka da shirye-shiryen wayar da kai kan illolin shan miyagun ƙwayoyi.
Haka kuma, hukumar ta gudanar da gwaje-gwajen shan miyagun ƙwayoyi 527, inda mutane 64 suka nuna alamun shan ƙwayoyi. Daga cikin waɗanda aka yi wa gwajin har da sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma, domin jaddada muhimmancin shugabanci mara alaƙa da miyagun ƙwayoyi a jihar.
A cikin haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da na sa ido, NDLEA Kano ta miƙa wasu shari’o’i ga ’Yan Sanda, Sojoji, DSS, NAFDAC da EFCC, waɗanda suka shafi laifuka irin su safarar makamai, ’yan bindiga, damfara, sata da kuma magungunan bogi.
Khadijah Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
