Connect with us

Labarai

NDLEA Kano Ta Kama Mutane 1,389 a 2025

Published

on

Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Ƙasa (NDLEA), reshen Kano, ta samu gagarumar nasara a shekarar 2025, inda ta kama mutane 1,389 da ake zargi da laifukan da suka shafi miyagun ƙwayoyi, tare da kwace kilogiram 7,773.06 na nau’o’in miyagun ƙwayoyi daban-daban, ciki har da tabar wiwi, da ta aljannu da kokin da a farci kasa da kuma ƙwayoyin maye na kwakwalwa.

Wadannan alkaluma, kamar yadda Jami’in Hulɗa da Jama’a na hukumar, Sadiq Muhammad Maigatari, ya bayyana, sun nuna irin gagarumar nasarar da rundunar ta samu ƙarƙashin jagorancin Kwamanda CN D.Y. Lawal wajen yaƙi da fatauci da shan miyagun ƙwayoyi a faɗin jihar Kano.

Daga cikin waɗanda aka kama, 1,346 maza ne yayin da mata 43 ne. Haka kuma rundunar ta samu hukunci 141 a kotu, lamarin da ya zama darasi ga masu shirin aikata irin waɗannan laifuka, inda manyan dillalan miyagun ƙwayoyi guda huɗu suka samu hukuncin da ya kai shekaru 33 a gidan yari gaba ɗaya.

Baya ga kamen mutane da gurfanarwa, rundunar ta kuma samu nasarar kwace wani gida da aka mallaka ta hanyar kudaden miyagun ƙwayoyi, tare da kwace wasu kadarori biyu na wucin gadi, yayin da shari’o’i 133 ke ci gaba da sauraro a Kotun Tarayya.

A fannin gyara da wayar da kan jama’a, NDLEA Kano ta ba da muhimmanci ga shirin farfaɗo da masu shaye-shaye da hulɗa da al’umma. Mutane 94 sun kammala shirye-shiryen gyaran hali na musamman, yayin da mutane 1,009 (ciki har da mata 28) suka samu shawarwari na gajeren lokaci.

Rundunar ta gudanar da kamfe 254 na yaƙi da miyagun ƙwayoyi a makarantu, kasuwanni da cibiyoyin al’umma, inda ta kai saƙon wayar da kai ga mutane 86,939 (maza 41,225 da mata 45,714) ta hanyar taruka da shirye-shiryen wayar da kai kan illolin shan miyagun ƙwayoyi.

Haka kuma, hukumar ta gudanar da gwaje-gwajen shan miyagun ƙwayoyi 527, inda mutane 64 suka nuna alamun shan ƙwayoyi. Daga cikin waɗanda aka yi wa gwajin har da sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma, domin jaddada muhimmancin shugabanci mara alaƙa da miyagun ƙwayoyi a jihar.

A cikin haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da na sa ido, NDLEA Kano ta miƙa wasu shari’o’i ga ’Yan Sanda, Sojoji, DSS, NAFDAC da EFCC, waɗanda suka shafi laifuka irin su safarar makamai, ’yan bindiga, damfara, sata da kuma magungunan bogi.

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara