Connect with us

Labarai

Najeriya Ta Kaddamar da Shafin Intanet Don Samun Bayanai Game da Ma’adinai

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet ranar Talata wanda zai bai wa masu zuba jari damar samun cikakkun bayanai game da ma’adanai da sauran albarkatun ƙasa.

Da yake ƙaddamar da shafin na intanet, Ministan Harkokin Ma’adinai na Nijeriya Dele Alake ya ce sun ɗauki matakin ne domin rage wahalhalun da masu zuba jari daga ƙasashen waje suke sha wurin samun bayanai game da ma’adanai da ƙasar take da su.

“A baya mutumin da ke son zuba jari sai ya zo Nijeriya da kansa kafin ya samu bayanan da yake buƙata, amma yanzu yana iya samun waɗannan bayanai a shafin intanet sannan ya yanke hukunci kan ko zai zuba jari,” a cewar Ministan.

Nijeriya ce kan gaba a albarkatun man fetur a Afirka, kuma tana da tarin arzikin sauran albarkatun ƙasa irin su zinare, kuza, tama da ƙarafa, kwal, farar ƙasa, da sauransu.

 kuma yana ɗauke da bayanai kan dukkan ma’adanain da Nijeriya take da su da jihohin da ake samunsu da ma duk wasu bayanai kan yadda za a zuba jari a kan su.

Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta sha alwashin bunƙasa fannin ma’adinan Nijeriya domin samun kuɗaɗen-shiga da rage dogaro da man fetur, tana mai cewa a halin da ake ciki wannan fanni ba ya samar da sama da kashi ɗaya na kuɗin-shigar ta.

A kwanakin baya ne Ma’aikatar Harkokin Ma’adinai ta Nijeriya ta gudanar da garambawul inda ta amince ta bai wa masu zuba jari kashi 75 na hannun-jarin kamfanin haƙar ma’adinai na ƙasar, tare da hana fitar da ma’adinan da ba a sarrafa ba, da haramta kamfanonin da ke haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara