Labarai
Matsalolinmu Sun Samo Asali Ne Daga Mulkin Mallaka — Obasanjo

Tsohon Shugaban Kasa, Olusegun Obasanjo, ya ce wasu daga cikin matsalolin da Najeriya ke fuskanta sun samo asali ne tun daga lokacin turawan mulkin mallaka.
Obasanjo, ya bayyana haka ne yayin gabatar da wata maƙalar littafi a ranar Asabar a Enugu.
“Duk tsarin da aka gabatar na tattalin arziki matukar babu gwamnatin mai manufa ga kuma gurgun tsari da ake fama da shi, wadannan abubuwan sai sun durkusar da tsarin.
“A matsayinmu na kasa, tarihinmu a bayyane yake mun sha fama da matsaloli a baya, kuma mun yi rashin damarmaki muhimmai,” in ji shi.
Tsohon shugaban ya ce akwai alaka tsakanin tattalin arziki da sauya tsarin siyasa a Najeriya.
Ya ce tarihin yadda aka samar da kundin tsarin mulkin Najeriya da tubalin da aka dora siyasar kasar sun nuna akwai wani gurbi da aka bari, wanda yake bukatar a cike shi.
A cewar Obasanjo akwai bukatar dora tubalin kasar nan a kan gwadabe mai tsari da zai yi daidai da mutanenta.
Kazalika, ya ce matuka ba samu jajirtattun shugabanni da za su tabbatar da tsarin da ya dace da kuma cike gibin matsalolin da Najeriya ta gada tun turawan mulkin mallaka, abu ne mai wuya a samu sauyin da ake muradi.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
