Labarai
Masu Fama Da Cutar Daji Sun Bukaci Gwamnatin Kano Basu Tallafi
Kungiyar masu fama da cutar daji ta Najeriya reshen jihar Kano, ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta bullo da tallafin kula da cutar a dukkan asibitocin gwamnati.
Shugaban kungiyar Salisu Yusuf ne ya yi wannan kira a yayin wani taron manema labarai na bikin ranar cutar Daji ta duniya tta shekarar 025.
Ya bukaci gwamnati da ta hada gwajin cutar Kansa, da jiyya, da kula da lafiyar jiki a cikin shirinta na ba da tallafin iwon lafiya.
Acewarsa matakin zai rage wa majinyata matsalar kudi, musamman wadanda suka fito daga iyalai masu karamin karfi.
Bugu da kari, kungiyar ta bukaci da a saka masu fama da cutar ta Daji da wadanda suka warke daga cutar a cikin shirin nan na Abba Care da aka kaddamar kwanan nan, wanda ke da nufin tallafa wa mutane masu raunu su 300,000.
Salisu Yusuf ya jaddada cewa cutar Kansa ta kasance babbar lalurar da ke bukatar kulawa cikin gaggawa. “Yawancin mutane na kokawa dangane da biyan kuɗin tantance masu dauke da cutar, da kudaden cigaba da samun kula da karbar magani idan aka gano suna dauke da cutar.
Kungiyar ta masu fama da cutar daji ta Najeriya ta yabawa kokarin gwamnatin jihar na inganta fannin kiwon lafiya, tare da yin kira ga masu hannu da shuni, da kungiyoyi masu zaman kansu, da cibiyoyin kiwon lafiya masu zaman kansu, da su tallafawa shirin kula da cutar Daji a Kano.
Ta jaddada kudirinta na bayar da shawarwarin sauye-sauyen tsarin da ke ba masu fama da cutar Kansa fifiko a Kano, ta hanyar wayar da kan jama’a da shirye-shiryen gano cutar da wuri.
Taken ranar Ciwon Daji ta Duniya na 2025, “United by Unique,” yana nuna mahimmancin aikin gamayya wajen yaƙar cutar Kansa.
Abdullahi Jalaluddeen
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
