Connect with us

Labarai

Mahajjata Sun Yabawa Gwamnatin Borno Da Hukumar Alhazai Bisa Basu Abinci Mai Inganci

Published

on

Alhazan Jihar Borno  sun yabawa hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) da gwamnatin jihar Borno bisa kyakkyawan tsarin shirin ciyarwa  a  Makka da Madina.

Alhazan da a halin yanzu suke shirin fara aikin Hajji a ranar Juma’a ta makon gobe, sun bayyana gamsuwarsu da inganci da wadataccen abinci da ake basu a kullum.

Wakilinmu Dauda Iliya wanda yanzu haka yake a garin Makka ya ruwaito cewa Alhazai 1,646 daga cikin 1,815 daga jihar sun kammala zamansu a Madina bayan sun yi ziyara a muhimman wurare.

Daya daga cikin mahajjatan  Hajia Fatima Usman ta ce ana basu abincin  mai gina jiki kuma irin wanda suka saba da shi.

Abincin da muke samu tun daga Madina zuwa nan Makka yana da kyau kwarai da gaske, muna jin dadin yadda ake bamu abincinmu na gargajiya da muka saba da shi, muna godiya ga Hukumar NAHCON da Gwamnatin Jihar Borno da suka tabbatar mana da samun wadataccen abinci a wannan lokacin.” in ji Hajiya Fatima.

Wani Alhaji mai suna Malam Abba Kyari, ya yabawa jami’an kwamitin ciyar da abinci da masu ba da abinci bisa kwarewa da kuma kula da Alhazai.

Kyari ya ce “Ma’aikatan da ke kula da abinci suna matukar bibiyar bukatunmu da korafe-korafenmu, idan akwai. Suna tabbatar da cewa an ba mu abinci a kan lokaci“.

Shugaban kwamitin ciyarwa  na tawagar Amirul Hajj Dr Ibrahim Adam ya bayyana jin dadinsa bisa yabon da Alhazan  ke yi, yana mai cewa hakan ya nuna irin jajircewar da gwamnatin jihar ta yi na kyautata rayuwar jami’ar ta da suke gudanar da aikin Hajjin.

Dangane da korafin da wasu maniyyatan ke yi na rasa abincin, Dr Ibrahim ya ce kwamitin ya bukaci masu kula da abincin da su kara samar da wadataccen abincin a lokacin karin kumallo da kuma abincin dare domin tabbatar da cewa  kowa ya samu.

Abin da muka sa a gaba shi ne tabbatar da kula da mahajjatan mu a yayin wannan tafiya ta ibada. Yabo daga alhazan Borno ya nuna cewa muna kan turbar da ta dace, kuma za mu ci gaba da hada hannu da NAHCON wajen tabbatar da wannan tsari,” in ji Dokta Ibrahim.

Wakilinmu ya ruwaito cewa, ana sa ran za a yi jigilar alhazan jihar Borno na karshe a kasa mai tsarki nan da kwanaki biyu masu zuwa.

Dauda Iliya

Labarai

Labarai11 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara