Connect with us

Labarai

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Published

on

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma wasu da aka takaita shigowarsu cikin ƙasa da darajarsu ta haura naira miliyan 478 a bana.

Mukaddashin Kwanturola na Kwastam a jihar, Mataimakin Kwanturola Najeem Ogundeyi, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai kan ayyukan rundunar a Ilorin.

Ya ce rundunar ta kuma samu kudaden shiga da suka haura naira biliyan 2.5 a cikin wannan lokaci da ake nazari, lamarin da ya ƙara tabbatar da rawar da take takawa wajen tallafa wa manufofin gwamnati na tattalin arziki.

A cewarsa, rundunar na da ƙudurin kare tattalin arzikin ƙasa tare da tabbatar da bin doka da oda.

Ogundeyi ya ce rundunar ba za ta bari jihar ta zama mafakar masu safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba, yana mai ƙara da cewa duk wanda ya yi ƙoƙarin tauye tattalin arzikin ƙasa ta hanyar fasa kwauri zai fuskanci matakin doka.

Mukaddashin Kwanturolan ya kuma nuna damuwa kan yadda ake ci gaba da safarar kaya ba bisa ƙa’ida ba duk da gargaɗin da ake yi, musamman shigo da shinkafar waje, wadda ke barazana ga manoman cikin gida.

Ogundeyi ya ce haramcin shigo da irin wannan shinkafa daga ƙasashen waje wani mataki ne na ƙarfafa masu noma a gida, samar da ayyukan yi da kuma bunƙasa samarda abinci.

Ya ƙara da cewa nasarar waɗannan ayyuka ta samu ne sakamakon bayanan sirri da kuma haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro.

Mukaddashin Kwanturolan ya kuma yi kira ga mazauna yankunan kan iyaka, ’yan kasuwa da sauran jama’a da su haɗa kai da hukumar domin kare masana’antun cikin gida, bunƙasa tattalin arzikin ƙasa da kuma samar da ci gaba mai ɗorewa.

Daga cikin kayayyakin da rundunar ta kama akwai motoci biyar da aka yi amfani da su, buhunan shinkafar waje guda 1,107, buhunan sukari da aka shigo da su 44, jarkoki 317 na man fetur (PMS), buhuna 120 na ma’adinin lithium da aka haƙo ba bisa ƙa’ida ba, da kuma ɗaruruwan tufafin gwanjo da sassan gyaran motoci.

ALI MUHAMMAD RABIU

Labarai

Labarai1 hour ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai1 hour ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai1 hour ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai2 hours ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai2 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara