Connect with us

Labarai

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda ya shiga tsakani a lamarin Walida wadda ake zargin wani jami’in Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) mai suna Ifeanyi Festus Onyewuenyi da yin garkuwa da ita.

Ƙungiyar ta bayyana cewa ceto yarinyar tare da jaririnta, waɗanda yanzu suke ƙarƙashin kulawar Gwamnatin Jihar Jigawa, wata babbar shaida ce da ke nuna ƙudirin Gwamna Namadi na kare rayuwa, mutunci da walwalar al’ummar jihar.

Shugaban ƙungiyar, Comrade Abubakar Babangida ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi a wani gangamin zanga-zangar goyon baya da aka gudanar a  garin Hadejia.

Comrade Abubakar ya sake jaddada kudirin ƙungiyarsu na ci gaba da mara wa gwamnatin Gwamna Namadi baya domin ganin an bi wannan shari’a har zuwa ƙarshe, tare da tabbatar da an yi wa waɗanda abin ya shafa adalci.

Sai dai masu zanga-zangar lumanar sun soki zanga-zangar da ƙungiyar ‘Hadejia Ina Mafita’ ta shirya, inda suka bayyana ta a matsayin wadda ke yaɗa bayanai marasa sahihanci da kuma ruɗar da jama’a, lamarin da ka iya haifar da rikici da hargitsi a cikin al’umma.

Sun kuma yi kira ga shugabannin Hadejia Ina Mafita da su riƙa yin taka-tsantsan yayin da suke magana ko sharhi kan irin waɗannan muhimman batutuwa, tare da gujewa siyasantar da su ko kuma ɓata sunan gwamnati.

Hakazalika, wata ƙungiyar mata mai suna Jigawa Women Development Initiative ta gudanar da zanga-zangar lumana a Dutse, babban birnin jihar, domin nuna farin cikinsu kan rawar da Gwamna Namadi ya taka a matsayin uba da jagora a lamarin Walida Abdullahi.

Ƙungiyar matan ta bayyana matuƙar damuwarta kan abin da ya faru, tare da nuna tausayi ga wadda abin ya shafa da iyayenta bisa irin mummunan cin zarafin da ake zargin wanda ake tuhuma ya yi mata.

Don haka sun yi kira ga al’umma gaba ɗaya da su haɗa kai wajen nuna goyon baya ga Gwamnatin Jihar Jigawa domin tabbatar da cewa an yi adalci ga Walida Abdullahi.

Labarai

Labarai38 minutes ago

Tinubu Ya Nada Ibrahim Masari a Matsayin Mai Ba Shi Shawara Kan Harkokin Siyasa

Daga Bello Wakili Shugaban Ƙasa Bola Tinubu  ya naɗa Ibrahim Aminu Masari a matsayin Mai ba shi Shawara na Musamman...

Labarai1 hour ago

Kungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Wata ƙungiyar al’umma mai suna Hadejia Advocacy ta yaba wa Gwamnan  Jigawa, Umar Namadi, kan yadda...

Labarai7 hours ago

Ramadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsoro Tare da Tallafawa Marasa Galihu

Daga Yusuf Zubairu Kauru Sarkin Kauru da ke Jihar Kaduna, Alhaji Zakari Ya’u Shehu Usman, ya yi kira da a...

Labarai8 hours ago

Gwamnatin Jigawa Ta Sha Alwashin Bin Kadin Shari’ar Walida Abdulhadi

Daga Usman Muhammad Zaria  Gwamna Umar Namadi ya tabbatar da cewa Gwamnatin  Jigawa za ta bi sawun shari’ar sace ‘yar...

Labarai1 day ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi1 day ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai1 day ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Mafi Shahara