Connect with us

Labarai

Jirgin Farko Na Alhazan Jihar Kano Ya Isa Kasa Mai Tsarki

Published

on


Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya kaddamar da jirgin farko na maniyyata aikin hajjin bana a jihar.

 

Da yake jawabi yayin kaddamarwar, Gwamna Abba Kabir  ya bukaci maniyyatan da su kasance jakadu nagari tare da yin addu’a ga jihar da  Najeriya  baki daya.

Jirgin na farko na mahajjatan  Kano ya tashi ne daidai da karfe goma sha daya da minti arba’in da daya na safiyar yau dauke da  jimillar mutane 578, a jirgin sama na Max Air B747  inda suka nufi filin jirgin sama na Sarki Abdul-Aziz da ke Jiddah.

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Lamin Rabi’u Danbappa ya ce mahajjatan da ke  jirgin farkon sun fito ne daga kananan hukumomi hudu na jihar.

A cewarsa, karamar hukumar Gwale na da mahajjata 175, yayin da karamar hukumar Dala ke da alhazai 119, sai  karamar hukumar Ungogo tana da alhazai 106, ita kuma karamar hukumar Fagge na da mahajjata 135.

Ya kuma nuna jin jinjinawa Gwamna bisa karamcin da ya yi wa Alhazai da suka hada da tallafin kudin Hajji na Naira 500,000 kowanne, da karin kudin guzuri da ya kai sama da Naira miliyan 367, da karin Riyal 100  da aka bai wa dukkan maniyyatan.

 

Abdullahi Jalaluddeen

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara