Labarai
Jihar Zamfara: ‘Yan Sanda 390 Sun Sami Karin Girma
Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Zamfara, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya kawata jami’ai 390 da aka daga matsayinsu zuwa sabon mukami a rundunar.
An gudanar da bikin kawata jami’an ne a Hedikwatar Rundunar ‘Yan Sanda da ke Gusau, babban birnin jihar.

A cewar sanarwar da mai magana da yawun ‘yan sanda, DSP Yazid Abubakar, ya fitar, Kwamishinan ‘Yan Sanda ya taya sabbin jami’an murna tare da bukatar su tabbatar da cancantarsu da mukaman da aka ba su, ta hanyar rubanya kishin aiki, ladabi da kwarewa a ayyukansu.
Ya jaddada bukatar jami’an da su dage wajen yin aiki da jajircewa da kuma bayar da ingantaccen tsaro ga al’ummar Jihar Zamfara da Najeriya gaba ɗaya.

Daga cikin waɗanda suka sami karin girman akwai CSP Sani Kabiru da CSP Usman M. Nassarawa, waɗanda aka daga zuwa mukamin Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda (ACP).
“An daga jami’ai 30 daga matsayin Sifeto zuwa Mataimakin Sufiritandan ‘Yan Sanda (ASP II).” In ji Kwamishinan.

Ya ƙara da cewa, an daga jami’ai 242 daga Sajan zuwa Sufeta, sannan kuma an daga jami’ai 116 daga matsayin Kofur zuwa Sajan.
Da yake magana a madadin sabbin jami’an da aka daga matsayinsu, ACP Usman M. Nassarawa ya nuna godiya sosai ga Sufeto Janar na ‘Yan Sanda da Hukumar Kula da Ayyukan ‘Yan Sanda bisa amincewar da suka nuna a gare su.

Ya yi alkawarin cewa sabbin jami’an za su ci gaba da kiyaye manyan dabi’un aikin ‘yan sanda na Najeriya – wato gaskiya, jajircewa, ƙwarewa da amincewar jama’a – a hidimarsu ga ƙasa.
Daga Aminu Dalhatu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
