Connect with us

Labarai

Jihar Nasarawa Ta Tara Harajin Sama Da Naira Biliyan 16 A Wata 8

Published

on

Hukumar Haraji ta Nasarawa ta Hukumar Tara Haraji ta Jihar Nasarawa ta tara Naira biliyan 16 da Miliyan 500 daga watan Janairu zuwa Agustan 2025.

Shugaban Hukumar, Alhaji Ahmed Yakubu Mohammed, ne ya bayyana hakan lokacin da ya bayyana a gaban Kwamitin Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa kan Kuɗi da Kasafin Kuɗi, a wajen tantance rahoton aiwatar da kasafin kuɗi na zango na biyu na shekarar 2025 a Lafia.

Alhaji Ahmed Yakubu ya bayyana cewa hukumar ta samu nasara sosai, inda ya danganta nasarorin da suke samu ga goyon bayan da Gwamna Abdullahi Sule da kuma Majalisar Dokokin Jihar ke ba su.

Ya bayyana cewa kuɗaɗen da aka tara sun fito ne daga harkar ma’adinai, bankuna da kamfanonin gine-gine da sauran hanyoyi.

Shugaban hukumar ya tabbatar da cewa za su ci gaba da himma wajen nemo ƙarin hanyoyin da za su taimaka domin ƙara samun kuɗaɗe ga baitul-malin jihar.

Tun da farko, shugaban kwamitin, Alhaji Hudu A. Hudu, ya bayyana cewa an gudanar da binciken ne domin tantance yadda hukumar ta aiwatar da kasafin kuɗi na zango na biyu na shekarar 2025.

Ya yaba wa hukumar bisa ƙoƙarin da ta yi na ƙara kudaden shiga ga baitul-mali na jihar.

Alhaji Hudu ya shawarci hukumar da ta ƙara himma wajen samar da ƙarin kuɗaɗe ga gwamnati.

Shugaban kwamitin ya yaba wa hukumar bisa nasarorin da suka cimma ya zuwa yanzu, tare da tabbatar musu da ƙarin haɗin kai da goyon bayan da zai taimaka musu su samu nasarori masu yawa nan gaba.

 

Daga Aliyu Muraki

 

 

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara