Labarai
Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar rigakafi tare da raba jaka da sauran kayayyaki ga maniyyatan aikin Hajjin 2024.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga wakilin gidan rediyon Najeriya a hedikwatar hukumar da ke Dutse, babban birnin jihar.
Ya yi bayanin cewa allurar rigakafin ga dukkan maniyyatan jihar na daga cikin sharuddan hukumar Saudiyya na bayar da biza.
A cewarsa, ana sa ran za a fara allurar rigakafi da rarraba kayayyakin a cibiyoyin bitar Alhazai da ke fadin kananan hukumomin jihar ashirin da bakwai.
Ya kara da cewa, ana ci gaba da gudanar da taron bita ga Maniyyata a dukkan cibiyoyin da aka kebe a fadin jihar.
Ya ce, hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta kammala dukkan shirye-shiryen jigilar Alhazan jihar zuwa kasa mai tsarki cikin sauki.
Ya kuma bayyana cewa hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ce ta tsara jigilar maniyyatan jihar ta bana, inda ta bai wa kamfanin Max Air damar jigilar Maniyyatan jihar zuwa kasar Saudiyya.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
