Labarai
Jami’an NDLEA A Kano Sun Kama Wata Tirela Dauke Da Miyagun Kwayoyi Daga Legas
Jami’an Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) shiyar Kano sun kama kwalabe 8,000 na Akuskura, wani hadin ganyen magani da ake zargin na dauke da miyagun kwayoyi, tare da sinki 48 na tabar wiwi.
Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA a Kano, Sadik Muhammad Maigatari, ya bayyana cewa an cafke wani mutum mai shekaru 37 mai suna Ali Muhammad da ke da alaka da wannan laifi.
Ya bayyana cewa an kama kayan ne a Gadar Tamburawa, kan hanyar Zariya zuwa Kano, lokacin da jami’an suka dakatar da wata tirela dauke da kaya, da ta taso daga Legas zuwa Maiduguri.
Sadik ya kara da cewa, tirelar wacce take makare da Keke Napep, inda aka boye kayan a tsakanin kekunan da kuma karkashin tirelar, a wani rami na musamman da aka kera da katako domin boye miyagun kwayoyin.
“Jami’an sun gano kayan da aka boye ta hanyar bincike mai zurfi da kuma bayanan sirri.”
Ya ce yanzu haka ana tsare da wanda ake zargi tare da kayan da aka kama, inda ake ci gaba da bincike da gwaje-gwaje domin tantance sinadaran da ke cikin hadin da kuma gano sauran abokan huldarsa.
Sadik ya kara da cewa, kwamandan hukumar shiyar Kano, A. I. Ahmad, ya yaba da kokarin jami’ansa, tare da nuna godiya ga goyon bayan shugaban hukumar, Brig. Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), wanda ke karfafa jami’an wajen fatattakar masu safarar miyagun kwayoyi.
Hukumar ta kuma shawarci al’umma da su kasance masu sa ido, tare da bayar da rahoton duk wasu kaya ko aiki da ake zargin na da nasaba da miyagun kwayoyi ga ofishin NDLEA mafi kusa ko kuma ga sauran jami’an tsaro.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
