Connect with us

Labarai

Jami’an NDLEA A Kano Sun Kama Wata Tirela Dauke Da Miyagun Kwayoyi Daga Legas

Published

on

Jami’an Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) shiyar Kano sun kama kwalabe 8,000 na Akuskura, wani hadin ganyen magani da ake zargin na dauke da miyagun kwayoyi, tare da sinki 48 na tabar wiwi.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA a Kano, Sadik Muhammad Maigatari, ya bayyana cewa an cafke wani mutum mai shekaru 37 mai suna Ali Muhammad da ke da alaka da wannan laifi.

Ya bayyana cewa an kama kayan ne a Gadar Tamburawa, kan hanyar Zariya zuwa Kano, lokacin da jami’an suka dakatar da wata tirela dauke da kaya, da ta taso daga Legas zuwa Maiduguri.

Sadik ya kara da cewa, tirelar wacce take makare da Keke Napep, inda aka boye kayan a tsakanin kekunan da kuma karkashin tirelar, a wani rami na musamman da aka kera da katako domin boye miyagun kwayoyin.

Jami’an  sun gano kayan da aka boye ta hanyar bincike mai zurfi da kuma bayanan sirri.”

Ya ce yanzu haka ana tsare da wanda ake zargi tare da kayan da aka kama, inda ake ci gaba da bincike da gwaje-gwaje domin tantance sinadaran da ke cikin hadin da kuma gano sauran abokan huldarsa.

Sadik ya kara da cewa, kwamandan hukumar shiyar  Kano, A. I. Ahmad, ya yaba da kokarin jami’ansa, tare da nuna godiya ga goyon bayan shugaban hukumar, Brig. Janar Mohamed Buba Marwa (mai ritaya), wanda ke karfafa jami’an wajen fatattakar masu safarar miyagun kwayoyi.

Hukumar ta kuma shawarci al’umma da su kasance masu sa ido, tare da bayar da rahoton duk wasu kaya ko aiki da ake zargin na da nasaba da miyagun kwayoyi ga ofishin NDLEA mafi kusa ko kuma ga sauran jami’an tsaro.

 

Daga Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara