Labarai
Hukumar Shige da Fice ta Kasa ta Ceto Mutane 22 da Aka Yi Yunkurin Safararsu
Daga Isma’il Adamu
Hukumar Shige da Fice ta kasa ta ceto mutane 22 da aka yi yunkurin safararsu, a yankin kan iyakar Zango da ke Jihar Katsina.
Kwamandan Hukumar na Rundunar Iyakokin Jibia, Haruna Zakirai ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Daura.
Ya bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne a sansanin sintirin jami’an hukumar da ke Daura, bayan samun bayanan sirri daga wasu mazauna yankunan da ke kan iyaka, waɗanda yi zargin wadansu mutane yayin da suke ƙoƙarin tsallakawa da waɗanda abin ya shafa zuwa ƙetare.
Zakirai ya ce jami’ai da ma’aikatan sansanin sintiri na Daura sun gaggauta ɗaukar mataki, inda suka tare waɗanda mutanen a wani kango a ƙauyen Maibara da ke Ƙaramar Hukumar Zango ta jihar.
Ya bayyana cewa mutanen da aka ceto sun haɗa da mata 11 da maza 11, masu shekaru tsakanin 17 zuwa 35, waɗanda suka fito daga jihohi daban-daban na ƙasar nan da suka haɗa da Lagos, Osun, Rivers, Kwara, Katsina, Imo, Ondo, Benue, da Babban Birnin Tarayya Abuja.
“Binciken farko ya nuna cewa ana safarar mutanen ne zuwa ƙasar Libya, daga nan kuma zuwa Turai, inda aka yaudare su da alkawarin samun ingantacciyar rayuwa.
“Wannan dabara ce da ƙungiyoyin safarar mutane ke yawan amfani da ita wajen ruɗar mutanen da ba su sani ba. Muna kira ga al’umma da su guji fadawa wannan tarko, domin a koda yaushe Hukumar Shige da Fice tana shirye wajen tarwatsa irin waɗannan ƙungiyoyi da kuma ceto mutanen da ake yunkurin safarar su,” in ji shi.
Zakirai ya ƙara da cewa akwai ɗan ƙasar Togo daga cikin mutanen da aka ceto, wanda za a mayar da shi ƙasarsa bayan kammala bincike. Ya kuma ce a yanzu haka hukumar na neman shugaban ƙungiyar masu safarar wanda aka sani da suna “Cargo” ruwa a jallo, wanda ya tsere lokacin da ake kokarin kama ‘yan ƙungiyar ta sa.
Ya jaddada ƙudirin Hukumar Shige da Fice ta kasa, na yaƙi da safarar mutane, ƙaura ba bisa ƙa’ida ba, da laifukan ketare iyaka, tare da roƙon al’umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai kan duk wani da ake zargi da safarar mutane.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
