Connect with us

Labarai

Hukumar Shige da Fice ta Kasa ta Ceto Mutane 22 da Aka Yi Yunkurin Safararsu

Published

on

Daga Isma’il Adamu 

Hukumar Shige da Fice ta kasa ta ceto mutane 22 da aka yi yunkurin safararsu,  a yankin kan iyakar Zango da ke Jihar Katsina.

Kwamandan Hukumar na Rundunar Iyakokin Jibia, Haruna Zakirai ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Daura.

Ya bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne a sansanin sintirin jami’an hukumar da ke Daura, bayan samun bayanan sirri daga wasu mazauna yankunan da ke kan iyaka, waɗanda yi zargin wadansu  mutane yayin da suke ƙoƙarin tsallakawa da waɗanda abin ya shafa zuwa ƙetare.

Zakirai ya ce jami’ai da ma’aikatan sansanin sintiri na Daura sun gaggauta ɗaukar mataki, inda suka tare waɗanda mutanen a wani kango a ƙauyen Maibara da ke Ƙaramar Hukumar Zango ta jihar.

Ya bayyana cewa mutanen da aka ceto sun haɗa da mata 11 da maza 11, masu shekaru tsakanin 17 zuwa 35, waɗanda suka fito daga jihohi daban-daban na ƙasar nan da suka haɗa da Lagos, Osun, Rivers, Kwara, Katsina, Imo, Ondo, Benue, da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Binciken farko ya nuna cewa ana safarar mutanen ne zuwa ƙasar Libya, daga nan kuma zuwa Turai, inda aka yaudare su da alkawarin samun ingantacciyar rayuwa.

“Wannan dabara ce da ƙungiyoyin safarar mutane ke yawan amfani da ita wajen ruɗar mutanen da ba su sani ba. Muna kira ga al’umma da su guji fadawa wannan tarko, domin a koda yaushe Hukumar Shige da Fice tana shirye wajen tarwatsa irin waɗannan ƙungiyoyi da kuma ceto mutanen da ake yunkurin safarar su,” in ji shi.

Zakirai ya ƙara da cewa akwai ɗan ƙasar Togo daga cikin mutanen da aka ceto, wanda za a mayar da shi ƙasarsa bayan kammala bincike. Ya kuma ce a yanzu haka hukumar na neman shugaban ƙungiyar masu safarar wanda aka sani da suna “Cargo” ruwa a jallo, wanda ya tsere lokacin da ake kokarin kama ‘yan ƙungiyar ta sa.

Ya jaddada ƙudirin Hukumar Shige da Fice ta kasa, na yaƙi da safarar mutane, ƙaura ba bisa ƙa’ida ba, da laifukan ketare iyaka, tare da roƙon al’umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai kan duk wani da ake zargi da safarar mutane.

 

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara