Connect with us

Labarai

Hukumar Shige da Fice ta Kasa ta Ceto Mutane 22 da Aka Yi Yunkurin Safararsu

Published

on

Daga Isma’il Adamu 

Hukumar Shige da Fice ta kasa ta ceto mutane 22 da aka yi yunkurin safararsu,  a yankin kan iyakar Zango da ke Jihar Katsina.

Kwamandan Hukumar na Rundunar Iyakokin Jibia, Haruna Zakirai ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudana a Daura.

Ya bayyana cewa an gudanar da aikin ceton ne a sansanin sintirin jami’an hukumar da ke Daura, bayan samun bayanan sirri daga wasu mazauna yankunan da ke kan iyaka, waɗanda yi zargin wadansu  mutane yayin da suke ƙoƙarin tsallakawa da waɗanda abin ya shafa zuwa ƙetare.

Zakirai ya ce jami’ai da ma’aikatan sansanin sintiri na Daura sun gaggauta ɗaukar mataki, inda suka tare waɗanda mutanen a wani kango a ƙauyen Maibara da ke Ƙaramar Hukumar Zango ta jihar.

Ya bayyana cewa mutanen da aka ceto sun haɗa da mata 11 da maza 11, masu shekaru tsakanin 17 zuwa 35, waɗanda suka fito daga jihohi daban-daban na ƙasar nan da suka haɗa da Lagos, Osun, Rivers, Kwara, Katsina, Imo, Ondo, Benue, da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Binciken farko ya nuna cewa ana safarar mutanen ne zuwa ƙasar Libya, daga nan kuma zuwa Turai, inda aka yaudare su da alkawarin samun ingantacciyar rayuwa.

“Wannan dabara ce da ƙungiyoyin safarar mutane ke yawan amfani da ita wajen ruɗar mutanen da ba su sani ba. Muna kira ga al’umma da su guji fadawa wannan tarko, domin a koda yaushe Hukumar Shige da Fice tana shirye wajen tarwatsa irin waɗannan ƙungiyoyi da kuma ceto mutanen da ake yunkurin safarar su,” in ji shi.

Zakirai ya ƙara da cewa akwai ɗan ƙasar Togo daga cikin mutanen da aka ceto, wanda za a mayar da shi ƙasarsa bayan kammala bincike. Ya kuma ce a yanzu haka hukumar na neman shugaban ƙungiyar masu safarar wanda aka sani da suna “Cargo” ruwa a jallo, wanda ya tsere lokacin da ake kokarin kama ‘yan ƙungiyar ta sa.

Ya jaddada ƙudirin Hukumar Shige da Fice ta kasa, na yaƙi da safarar mutane, ƙaura ba bisa ƙa’ida ba, da laifukan ketare iyaka, tare da roƙon al’umma da su rika bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai kan duk wani da ake zargi da safarar mutane.

 

 

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara