Labarai
Hukumar NOA Ta Bukaci Al’umma Su Kara Hakuri Da Kaunar Juna
Hukumar wayar da kan jama’a ta kasa NOA, ta yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi amfani da wannan lokaci na watan Ramadan wajen tunanin abubuwan da za su amfani kasa baki daya.
Kodinetan hukumar na jihar Jigawa Mallam Ahmed Tijjani Ibrahim
ya yi wannan kiran a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.
Malam Ahmed Tijjani ya kuma yi kira ga al’ummar Musulmi da su yi addu’ar zaman lafiya, da tsaro da ci gaban jihar da kasa baki daya.
Ya bayyana watan Ramadan a matsayin wata mai alfarma da ake son musulmi su kara kusanta ga Allah SWT, ta hanyar tsarkake zukatansu.
Don haka Tijjani ya umarce su da su zama ’yan uwan juna, su kasance masu hakuri da kamun kai, da tausaya wa marasa galihu a cikin al’umma.
Ya kara da cewa, NOA za ta bi sahun gwamnatin jihar domin sanya ido da kuma lura da al’amuran da ke gudana a watan Ramadan na wannan shekara domin tabbatar da ganin komi ya tafi yadda ake bukata.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai13 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
