Connect with us

Kasuwanci

Hukumar Kwastam Ta Kama Kilo 420 Na Bawon Dabbar Dankunya A Kano

Published

on

Hukumar Kwastam ta Najeriya reshen Kano/Jigawa, ta kama wani adadi mai yawa na bawon dabbar Dankunya wato pangolin mai nauyin kilogiram 420 a wata unguwa da ke cikin birnin Kano.

 

Shugaban Hukumar Kwastam, Abubakar Dalhat ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a Kano.

Ya ce an gudanar da aikin ne a ranar 16 ga Yuli, 2025, sakamakon hadin gwiwa tsakanin jami’an kwastam da sauran hukumomin da abin ya shafa. Abubakar Dalhat ya bayyana cewa, an gudanar da wannan aiki ne da nufin yakar haramtacciyar kasuwancin namun daji da sauran laifukan da suka hada da kare albarkatun kasa da Najeriya ke da kima ga al’umma na yanzu da kuma masu zuwa.

 

Ya bayyana cewa kama wannan bawondabbar pangolin ba wai kawai yana wakiltar lalata hanyoyin masu laifi ba ne, har ma yana aike da sako mai ƙarfi ga masu fataucin namun daji cewa ba za a amince da aikata laifuka kan namun daji ba a Najeriya ko kuma a duk faɗin duniya.

 

“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare muhallinmu da namun daji kamar yadda sashi na 55 na dokar hukumar kwastam ta Najeriya ta 2023 ta bukata.”

 

 

Shugaban Kwastam din ya yabawa Kwanturola Janar na Hukumar Kwastam, Bashir Adewale Adeniyi MFR, bisa jajircewarsa da goyon bayansa wajen gudanar da wannan aiki.

 

 

Ya kuma gode wa abokan huldar kasa da kasa, irin su ofishin hulda da kasa da kasa na Yanki da kuma Focus Conservation, saboda taimakon da suke bayarwa.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara