Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Jajantawa Iyalan Wadanda Suka Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa

Published

on

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana alhininta kan mummunan hatsarin jirgin ruwa da ya auku ranar Juma’a a Nasarawan Kifi, da ke Gundumar Birnin Tudu ta Karamar Hukumar Gummi, wanda ya yi sanadiyar mutuwar wasu mutane da ke kokarin tserewa daga harin ’yan bindiga.

A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Yaɗa Labarai da Al’adu na jihar, Mahmud Muhammad Dantawasa, ya fitar, ya ce rahotannin farko sun nuna cewa jirgin ruwan ya ɗauki fasinja ne fiye da ƙima, wanda hakan ya jawo kifewar sa a tsakiyar hanya, inda ya  haddasa asarar rayuka da dama.

Ya bayyana cewa ana ci gaba da aikin ceto da binciko wadanda suka bace, inda ƙungiyoyin gaggawa ke aiki tare da shugabannin al’umma domin tantance adadin mutanen da suka ɓace da kuma bayar da agajin gaggawa ga waɗanda suka tsira.

A madadin Gwamnatin Jihar Zamfara, muna mika ta’aziyyar mu ga iyalan waɗanda suka rasu, tare da roƙon Allah ya jikansu da rahama,” In ji sanarwar.

Mahmud Dantawasa ya ƙara da cewa gwamnatin jihar na aiki don ganin iyalan da abin ya shafa sun samu tallafi da agaji cikin gaggawa.

A cewarsa, Gwamna Dauda Lawal ya umurci jami’an tsaro da su ƙara kaimi wajen gudanar da ayyuka a yankin, domin hana ƙarin hare-haren ’yan bindiga da kuma kare rayukan mazauna ƙauyukan da abin ya shafa.

Ya sake tabbatar da aniyar gwamnatin Zamfara na kawo ƙarshen matsalar ’yan bindiga.

 

Daga Aminu Dalhatu

 

 

 

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara