Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Bada Buhunan Abinci 36,000 Ga Jihar Borno

Published

on

Gwamnatin tarayya ta baiwa gwamnatin jihar Borno tallafin buhunan abinci dubu talatin da shida da dari biyu da goma sha hudu masu nauyin kilogiram hamsin.

Da take gabatar da kayayyakin ga Gwamnan Jihar Farfesa Babagana Zulum, Darakta Janar ta Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA, Hajiya Zubaida Umar ta ce kayayyakin na daga cikin  tan dubu arba’in da biyu  na hatsi da aka fitar daga runbun gwamnati.

Shugabar hukumar wacce darakta janar na shiyyar Arewa maso Gabas, Malam Yakubu Sulieman, ya wakilce ta, ta bayyana cewa bada tallafin kayan abinci na daga cikin shirin rage tasirin tabarbarewar tattalin arzikin da ake fama da shi a yankin.

Shugaban kasa ya amince da fitar da kayayyakin abinci har ton 42,000 daga runbun gwamnatin tarayya da ke karkashin kulawar ma’aikatar noma da samar da abinci ta, a don haka mun zo ne domin mika kayayyakin ga gwamnatin jihar Borno inda za ta  raba ga wadanda suka cancanta”.

A jawabinsa, Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya jinjinawa  gwamnatin tarayya bisa wannan karamci ga al’ummar jihar, musamman wadanda rikicin Boko Haram ya shafa.

Ya kuma baiwa shugaban kasa da hukumar bada agajin gaggawa ta kasa tabbacin cewa za a raba kayan abincin da aka bayar ga marasa galihu a jihar.

Ina kuma tabbatar muku da cewa ba za a samu karkatar da kayayyakin a jihar Borno ba, za a raba bisa cancanta ga al’ummar jihar.” Inji Zulum.

Gwamna Zulum ya kuma yabawa gwamnatin tarayya bisa bada gudunmawa a yunkurin da gwamnatin sa ke yi na sake tsugunar da wadanda rikici ya daidaita.

Shi ma a nasa jawabin,  Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA, Dokta Muhammed Barkindo ya ce za a ba da fifiko ga gidaje suka rasa mahaifinsu da marasa lafiya da kuma masu fama da lalurar nakasa.

Kayayyakin da aka bayar sun hada da buhunan Masara 11,880, buhunan dawa 19,440 da buhunan Gero 5,130.

 

Dauda Iliya 

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara