Kasuwanci
Gwamnatin Taraba Ta Shirya Rarraba Taraktoci Noma
Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas amince da tsarin kwamitin rabon tarakta a jihar.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Cif Timothy Kataps ya sanyawa hannu, kuma babban sakataren yada labaran gwamnan, Yusuf Sanda ya bayyanawa manema labarai.
Sanarwar ta ce kwamishinan noma da samar da abinci na jihar, Farfesa Nickolas Nemesson ne zai jagoranci kwamitin a matsayin shugaba.
Mambobin sun hada da shugaban RIFAN na jiha, Tanko Bobbo Andami, wakilan kungiyar kwadago, Mr. Gara Nuga daga kungiyar matasa ta kasa (NYCN), da majalisar mata ta kasa (NCWS).
Sauran mambobin kwamitin sun hada da Uchena Eschareturi, da Dr. Aminu Jauro Hassan, shugaban karamar hukumar Jalingo, mai wakiltar ALGON.
Sai dai Mista Samson Alhassan na ofishin sakataren gwamnatin jihar Taraba zai kasance sakataren kwamitin.
Sai dai har yanzu ba a bayyana ranar da za a fara rabon kayayyakin ba.
Sani Sulaiman/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
