Labarai
Gwamnatin Sakkwato Za Ta Kashe fiye da Naira Miliyan 200 Wajen Gyara Tashar Talabijin Ta Kasa NTA
Majalisar zartaswar jihar Sokoto a karkashin jagorancin Gwamna Ahmed Aliyu ta amince da kashe kudade wajen ayyuka a sassa daban daban nufin tabbatar da amana da aka dora wa gwamnati.
Da yake karin haske ga manema labarai yayin taron da ya saba gudanarwa, kwamishinan yada labarai Alh. Sambo Bello Danchadi ya ce majalisar ta amince da bayar da kwangilar gina dakin kwanan dalibai mai hawa daya a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, da za a kasha naira miliyan dari hudu da tamanin da bakwai.
Alhaji Sambo Bello Danchadi ya ce majalisar ta kuma amince da gyaran sashen da aka kona na gidan talabijin ta Najeriya NTA Sokoto wanda kudinsa ya kai naira miliyan dari biyu da casa’in.
Danchadi, wanda ke tare da Kwamishinan Muhalli, Hon. Nura Dalhatu Tangaza, da kwamishinan ilimi mai zurfi, Farfesa Hamza Isa Maishanu, ya ce majalisar ta amince da naira miliyan dari tara da tamanin da biyar domin gyara titin Forces Avenue a wani yunkuri na sake fasalin hanyoyin jihar a jihar.
An kuma amince da naira miliyan dari biyu da ashirin da takwas don maye gurbin bututun ruwa dake karkashin kasa a kan hanyar Sultan Atiku-Aliyu Jedo don magance matsalar magudanar ruwa da ambaliyar ruwa.
Kwamishinan ya ci gaba da cewa, an ware naira miliyan dari da ashirin da biyu domin saye da rarraba itatuwa a fadin jihar da nufin yaki da kwararowar hamada da sauyin yanayi.
A bangaren addini kuma an amince da wasu naira miliyan dari da ashirin da biyu domin gyaran masallacin Juma’a na Minannata haka kuma an tsara kammala aikin nan da watanni shida tare da sauran amincewa.
NASIR MALALI
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
