Connect with us

Kasuwanci

Gwamnatin Kano Za Ta Yi Aiki Da Kasar Holland Akan Aikin Gona

Published

on

Gwamna Yusuf Ya Yi Haɗin gwiwa da Gwamnatin Ƙasar Netherland Ba ta Kan Tsaron Abinci, Sauyin Yanayi

 

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nemi kasar Netherland ta ba da goyon bayan diflomasiyya domin habaka noma da rage tasirin sauyin yanayi a jihar.

 

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana shirin kulla huldar diflomasiyya da gwamnatin kasar Holland, a lokacin da ya karbi bakuncin Ms Eva De Wit, Sakatariyar a Ofishin Jakadancin Netherland a Najeriya.

 

 

Gwamna Yusuf ya jaddada tasirin da Holland dake dashi a kan noma da sauyin yanayi a Turai.

 

 

Yayin da yake sanar da tawagar kasar Holland matakin da ya dauka game da alkaluman shan muggan kwayoyi da suka gada daga gwamnatin da ta shude, Gwamna Yusuf ya ce an bude cibiyoyin koyar da sana’o’i 24 domin samun kwarin guiwar matasa, su dogara da kansu.

 

Yusuf ya kara da cewa gwamnatin sa ta kuma gyara halayen wasu matasa kusan 713 da suka tsunduma kansu cikin ayyukan ‘yan daba ta hanyar hadin gwiwa da ‘yan sandan Najeriya domin dakile tashe-tashen hankula a jihar.

 

A nata bangaren, Ms De Wit wadda ita ma ta samu rakiyar Shugaban Ofishin Jakadancin, Hukumar Kula da ‘yan gudun Hijira ta Duniya, Mista Laurent De Boeck, ta yi alkawarin hada kai da gwamnatin jihar Kano a fannonin inganta rayuwar matasa, samar da abinci da kuma sauyin yanayi.

 

ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe

Labarai

Labarai18 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai19 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai20 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai2 days ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai3 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai3 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai3 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara