Kasuwanci
Gwamnatin Kano Za Ta Yi Aiki Da Kasar Holland Akan Aikin Gona

Gwamna Yusuf Ya Yi Haɗin gwiwa da Gwamnatin Ƙasar Netherland Ba ta Kan Tsaron Abinci, Sauyin Yanayi
Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya nemi kasar Netherland ta ba da goyon bayan diflomasiyya domin habaka noma da rage tasirin sauyin yanayi a jihar.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana shirin kulla huldar diflomasiyya da gwamnatin kasar Holland, a lokacin da ya karbi bakuncin Ms Eva De Wit, Sakatariyar a Ofishin Jakadancin Netherland a Najeriya.
Gwamna Yusuf ya jaddada tasirin da Holland dake dashi a kan noma da sauyin yanayi a Turai.
Yayin da yake sanar da tawagar kasar Holland matakin da ya dauka game da alkaluman shan muggan kwayoyi da suka gada daga gwamnatin da ta shude, Gwamna Yusuf ya ce an bude cibiyoyin koyar da sana’o’i 24 domin samun kwarin guiwar matasa, su dogara da kansu.
Yusuf ya kara da cewa gwamnatin sa ta kuma gyara halayen wasu matasa kusan 713 da suka tsunduma kansu cikin ayyukan ‘yan daba ta hanyar hadin gwiwa da ‘yan sandan Najeriya domin dakile tashe-tashen hankula a jihar.
A nata bangaren, Ms De Wit wadda ita ma ta samu rakiyar Shugaban Ofishin Jakadancin, Hukumar Kula da ‘yan gudun Hijira ta Duniya, Mista Laurent De Boeck, ta yi alkawarin hada kai da gwamnatin jihar Kano a fannonin inganta rayuwar matasa, samar da abinci da kuma sauyin yanayi.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai2 days agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai6 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai5 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
