Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano Ta Nada Ibrahim Garba Shugaban Tawagar ‘Yan Jarida A Hajjin Bana

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta amince da nadin Ibrahim Garba Shuaibu a matsayin shugaban tawagar ‘yan jaridu a aikin Hajjin 2024.

An bayyana hakan ne a yayin taron masu ruwa da tsaki na kaddamar da kwamitin gudanar da aikin Hajji na shekarar 1445AH/2024 a hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano da ke kwaryar birnin jihar.

Taron ya samu halartar ma’aikatan kafafen yada labarai da za su rika ba da rahoton abubuwan da ke gudana yayin  aikin Hajji  wanda   dubban maniyyata daga Najeriya da ma sauran sassan duniya baki daya ke halarta.

Shuaibu, wanda a halin yanzu shi ne sakataren yada labarai na mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya kware a harkar yada labarai da sadarwa.

Ya kuma taba zama tsohon shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa (NUJ) Correspondents Chapel reshen jihar Kano, da kuma wakilin jaridar This Day.

Nadin da aka yi masa a matsayin shugaban tawagar kafafen yada labarai wani gagarumin ci gaba ne, wanda ake sa ran zai yi amfani da  kwarewarsa wajen tafiyar da harkokin yada labarai na aikin hajji.

 

Sama da maniyyata 3,000 ne daga jihar Kano ake sa ran za su halarci aikin Hajjin 2024.

 

A ranar 15 ga watan Mayu ne daidake sa ran  fara jigilar maniyyata daga kasar nan zuwa kasa mai tsarki.

Gwamnatin jihar Kano ta shirya tsaf domin tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin kwanciyar hankali da nasara ga dukkan maniyyata, kuma nadin Shuaibu na daya daga cikin muhimman ayyukan.

 

Khadija Aliyu

Labarai

Labarai12 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara