Fasaha
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Shirin Tsaftar Muhalli Na Wata Wata Saboda Jarrabawar JAMB
A kokarinta na ganin an gudanar da jarrabawar hadin gwiwa ta hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB, gwamnatin jihar Kano ta dakatar da aikin tsaftar muhalli na watan Afrilun 2025.
An dauki wannan matakin ne bayan nazari da tuntubar masu ruwa da tsaki, a kokarin baiwa daliban jihar Kano damar rubuta jarabawarsu ba tare da wata matsala ba.
A wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar muhalli da sauyin yanayi, Ismail Garba Gwammaja ya fitar, ya ruwaito kwamishinan yana cewa.
“Dakatar na da nufin hana duk wani cikas da zai iya kawo cikas ga aikin jarrabawar da kuma tabbatar da cewa ‘yan dalibai za su iya zana jarabawarsu ba tare da wani shamaki ba, in ji Kwamishinan.
Kwamishinan Muhalli da Sauyin yanayi, Dr Dahiru M. Hashim, ya tabbatar wa mazauna jihar cewa dakatarwar na wucin gadi ne na wannan watan kawai, kuma za a ci gaba da aikin tsaftar mahalli ga baki daya a wata mai zuwa, Mayu 2025, a jihar.
Kwamishinan, ya yi kira ga mazauna yankin da su ba hukuma hadin kai da fahimtar dalilin da ya sa aka yanke wannan hukunci.
“Mun himmatu wajen tabbatar da tsafta da lafiya, kuma za mu yi aiki tukuru don ganin cewa ayyukan tsaftar muhalli ba su ci karo da wasu muhimman abubuwan da ke faruwa a jihar ba.”
Yayin da yake yabawa mazauna yankin bisa fahimtarsu da hadin kai da gwamnati mai ci, ya bukace su da su daina zubar da shara ba gaira ba dalili.
“kuma muna ba da hadin kai da ma’aikatan tsaftar muhalli don tabbatar da tsafta da lafiya a ko da yaushe, tare da yin addu’ar samun nasara ga daliban da za su zana jarabawar shiga jami’a ta JAMB ta hadin gwiwa.”
KHADIJAH ALIYU
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
