Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka

Published

on

A kokarinta na ci gaba da habbaka harkokin noma, Gwamnatin Jihar Jigawa ta ƙulla wata yarjejeniyar haɗin gwiwa da wasu manyan kamfanoni da suka yi fice a fannin dabarun bincike da samar da kayan aikin gona na zamani domin bunƙasa harkar noma a jihar.

Mai magana da yawun Gwamnan Jihar Jigawa, Hamisu Mohammed Gumel ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a Dutse, babban birnin Jihar Jigawa.

Ya yi bayanin cewar, an ƙulla wannan yarjejeniyar haɗin gwiwa ne a wani zaman tattaunawa da aka yi a birnin Washington DC na Kasar Amurka tsakanin tawagar ƙwararru daga Jihar Jigawa ƙarƙashin jagorancin Gwamna Umar Namadi da kuma wakilan shugabannin kamfanonin da abin ya shafa.

A cewar sa, tattaunawar da ta gudana tsakanin ɓangarorin biyu ta ta’allaƙa ne kan yadda za a samar da kuma bunƙasa dabarun noma tare da shigar da matasa cikin harkar noma domin ganin an ɗaga matsayi da inganta rayuwar al’ummar jihar Jigawa ta hanyar noma.

Hamisu Mohammed Gumel ya yi nuni da cewar, daga cikin kyawawan sakamakon da wannan tattaunawar ta haifar shine ƙuduri na haɗin gwiwa da aka zartas na samar da wani shiri da a cikinsa za a siyo tarakta guda 300.

Yana Mai cewar nan bada jimawa ba za’a kawo su don ci gaba da inganta harkar noma a jihar ta Jigawa.

Ya ce wannan zai taimaka matuƙa wajen bunƙasar samun amfanin gona mai kyau da inganci a tsakanin ƙananan manoman jihar.

Hamisu Mohammed ya ce a ƙarƙashin wannan shiri ana sa ran za a horas da matasa sama da dubu daya da dari biyu kan harkar kasuwancin sayarwa da ba da hayar kayan aikin gona da kuma sarrafawa tare da gyaran taraktoci da sauran na’urorin aikin da za a samar.

Babbar manufar wannan shiri ita ce jawo matasa su shiga cikin harkar noma, wanda a yau ita ce hanyar samar da isasshen abinci da bunƙasar tattalin arziki a jiha da kuma ƙasa baki ɗaya.

Kazalika, yace hakan wani ɓangare na manufofin da Gwamna Umar Namadi ya ƙuduri aiwatarwa don inganta fannin noma da sauran fannonin rayuwa a Jigawa da ya zayyana a cikin ƙudurori 12 na gwamnatinsa.

Da yake magana kan ƙulla wannan haɗin gwiwa, Gwamna Umar Namadi ya ƙara jaddada muhimmancin yin amfani da dabaru da kayan aikin gona na zamani tare da jawo matasa cikin harkar, domin ta hakan ne za a tabbatar an inganta wannan fannin na noma a nan gaba.

Namadi, ya ce gwamnatin sa za ta ci gaba da tallafawa manoma, musamman matasa da a yanzu suka fara ganin muhimmancin wannan fanni, ta hanyar samar da kayan aiki da dabarun noma na zamani don ci gaban al’umma.

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara