Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura

Published

on

Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta ci gaba da tallafawa harkokin koyo da koyarwa a Jami’ar Fasaha ta Gwamnatin Tarayya dake karamar hukumar Babura.

 

Mataimakin Gwamnan jihar, Injiniya Aminu Usman ya bayyana haka a lokacin da ya karbi bakuncin sabon shugaban gudanarwar jami’ar Oba Ajigbade Gbadegesin Ogunoye Olowo na Owo na uku a ofishinsa dake Dutse babban birnin jihar.

 

Mataimakin Gwamnan wanda ya sami wakilcin Shugaban Ma’aikata na jihar Alhaji Muhammed Dagacheri, yace Gwamna Umar Namadi ya bada umarnin gina gidaje da kuma samar da kayayyakin koyo da koyarwa domin baiwa malaman jami’ar kwarin gwiwar gudanar da ayyukan su.

 

Kazalika, ya bada tabbacin gwamnatin jihar na ci gaba da tallafawa jami’ar domin amfanin ‘yan jiha da ma kasa baki daya.

 

A jawabin sa, sabon shugaban gudanarwar jami’ar, basarake Oba Ajigbade ya yabawa gwamnatin jihar Jigawan bisa tallafawa jami’ar a koda yaushe.

 

A don haka, ya bada tabbacin ciyar da Jami’ar gaba a matsayinsa na shugaban gudanarwarta na farko, tare da neman hadin kan gwamnatin da ma al’ummar jihar domin kwalliya ta biya kudin sabulu.

Tun farko a jawabin sa, shugaban jami’ar Farfesa Sabo Birnin Kudu yace sun zo ofishin mataimakin Gwamnan ne domin gabatar da sabon shugaban gudanarwar jami’ar da kuma godewa gwamnatin jihar bisa tallafin da take bai wa jami’ar.

 

Yana mai cewar jami’ar ta na da yawan dalibai dubu daya da ma’aikata 180 da kuma Kwasa-kwasai guda goma sha takwas da take gudanarwa.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara