Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Gwangwaje Kungiyoyin Wasanni Da Kyaututtuka

Published

on

Kwamishinan yada labarai  matasa da wasanni na jihar Jigawa, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bada kyautuka ga kungiyoyin wasanni da suka yi fice a gasar wasan cikar Gwamna Mallam Umar Namadi shekara guda akan karagar mulki.

An gudanar da bikin karramawar ne a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake Dutse.

Alhaji Sagir Musa Ahmed yace bada kyautukan na daga cikin alkawarin da Gwamna Umar Namadi ya yi a lokacin wasan karshe na murnar cikar gwamna shekara guda a kan karagar mulki.

An bada kyautar naira miliyan 4 ga kulob din kwallon kafa na Dutse da ya zo na farko,  sai kulob din Birnin Kudu wanda ya yi na biyu da ya samu kyautar naira miliyan 3.

Lautai united wadda tazo na uku ta sami kyautar naira miliyan 2.

Kazalika, an bada kyautuka ga zakarun wasannin langa da dambe da kokuwa da wasan kwando da wasan kwallon hannu da dai sauran su.

A jawabinsa, kwamishina Sagir Musa Ahmed ya ce hakan ya nuna cewar an dawo da ruhin wasanni a Jigawa

Ya kuma yi bayani akan kokarin da ake na habbaka  harkokin wasanni a jihar.

Ya ce suna tattaunawa da kwamishinonin ilmi domin yin amfani da makarantu wajen farfado da harkar wasanni.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara