Labarai
Gwamnatin Jigawa Ta Gwangwaje Kungiyoyin Wasanni Da Kyaututtuka
Kwamishinan yada labarai matasa da wasanni na jihar Jigawa, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya bada kyautuka ga kungiyoyin wasanni da suka yi fice a gasar wasan cikar Gwamna Mallam Umar Namadi shekara guda akan karagar mulki.
An gudanar da bikin karramawar ne a dakin taro na Sir Ahmadu Bello dake Dutse.
Alhaji Sagir Musa Ahmed yace bada kyautukan na daga cikin alkawarin da Gwamna Umar Namadi ya yi a lokacin wasan karshe na murnar cikar gwamna shekara guda a kan karagar mulki.
An bada kyautar naira miliyan 4 ga kulob din kwallon kafa na Dutse da ya zo na farko, sai kulob din Birnin Kudu wanda ya yi na biyu da ya samu kyautar naira miliyan 3.
Lautai united wadda tazo na uku ta sami kyautar naira miliyan 2.
Kazalika, an bada kyautuka ga zakarun wasannin langa da dambe da kokuwa da wasan kwando da wasan kwallon hannu da dai sauran su.
A jawabinsa, kwamishina Sagir Musa Ahmed ya ce hakan ya nuna cewar an dawo da ruhin wasanni a Jigawa
Ya kuma yi bayani akan kokarin da ake na habbaka harkokin wasanni a jihar.
Ya ce suna tattaunawa da kwamishinonin ilmi domin yin amfani da makarantu wajen farfado da harkar wasanni.
Usman Mohammed Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
