Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Bada Tallafin Littattafan Ilmantar Da Alhazai Aikin Hajji

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa ta baiwa hukumar jin dadin Alhazai ta jihar da kuma hukumar kula da ilimin addinin musulunci gudunmawar kwafin litattafai dubu biyar mai suna “GUZURIN MAHAJJATA” da nufin karfafawa maniyyata ilimi da shirye-shiryen tafiya kasa  mai tsarki.

Da yake mika littattafan ga shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai da Babban Sakatare na Hukumar Ilimi ta Musulunci, Alhaji Ahmed Umar Labbo da Dokta Mubarak Abdulwahab Hassan, Sakataren Gwamnatin Jiha, Malam Bala Ibrahim ya ce wannan karimcin na daga cikin kudirin gwamnatin jihar na  don sauƙaƙa tafiya da gudanar da aikin Hajjin cikin sauki ga Mahajjatan jihar.

Malam Bala Ibrahim ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na samar da dukkanin abubuwan da suka dace ga maniyyatan.

Ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta yanke shawarar daukar nauyin buga kwafin litattafai guda 5,000 domin karfafawa maniyyata ilimi da kuma shirye-shiryen tafiyarsu kasa mai tsarki.

A jawabinsa, shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya gode wa gwamnati bisa wannan karimcin.

Shugaban, wanda Daraktan Yada Labarai na Hukumar Malam Murtala Abdu Babura ya wakilta, ya yaba wa Gwamna Umar Namadi bisa  bayar da tallafin Naira miliyan daya ga Alhazan jihar.

A lokacin da yake bitar littafin, Malam Mahmud Yunusa ya bayyana cewa littafin yana da matukar muhimmanci ga Jagorar aikin hajji, inda ya ce  yana da kyau Alhazan  su karanta shi, da ma  masu son koyon Fiqhu da ladubban aikin Hajji.

Malam Mahmud Yunusa ya yabawa marubucin littafin aikin, tare da godewa Gwamna Umar Namadi bisa jajircewarsa na ci gaba da kyautata jin dadin alhazai a kowane lokaci.

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai2 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai23 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Mafi Shahara