Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Ta Bada Takardar Kama Aiki Ga Malaman Makarantu Sama Da 3000

Published

on

 

Gwamna Umar Namadi ya bayar da takardun kama aiki na dindindin ga malaman makarantu 3,143, tare da daukar ma’aikatan wucin gadi 2,445 a jihar.

Da yake jawabi a wajen bikin bayar da takardun kama aikin da aka gudanar a dakin taro na Malam Aminu Kano Triangle da ke Dutse, ya bayyana cewa, wannan gagarumin aikin na daga cikin tsare-tsare na samun nasarar aiwatar da manufofinsa guda 12.

Ya bayyana cewa babu wata manufa ta gwamnati da za a iya aiwatar da ita yadda ya dace ba tare da isasshen horo da kwararrun ma’aikata ba.

Ajandarmu guda 12 da aka tsara don ganin jihar Jigawa ta bunkasa sun hada da samar da ilimi mai inganci ga daukacin yara a jihar, kuma don samun nasarar haka ya zama wajibi mu kara samar da kwararrun malamai.”

Ya ci gaba da bayanin cewa, a kokarin cimma burinsu na samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya ga daukacin ‘yan jihar, magance yawaitar mace-macen yara da mata masu juna biyu, samar da lafiyar al’umma  da walwala, gwamnatin jihar ta tura  dalibai sama da 120 zuwa  kasashen Cyprus da Indiya domin karatun aikin likitanci.

A cewarsa, gwamnati mai ci ta kaddamar da gina makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta naira biliyan 5 da rabi, inda a yanzu ta bayar da aikin yi ga ma’aikatan lafiya 1,005 da suka hada da likitoci da kananan ma’aikata.

Gwamnan ya yi nuni da cewa, noma na daya daga cikin muhimman sassa na ajandarsa guda 12, wanda aka kudiri aniyar samar da ayyukan yi, kawar da fatara, samar da abinci, da kuma ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

Haɓaka amfani da fasahar noma ta zamani da samar da kayan aikin gona na zamani da araha ga manoma yana da matuƙar mahimmanci wajen cimma burin da aka sa a gaba, kuma bisa la’akari da hakan a yau muna gabatar da tayin aiki ga ma’aikatan aikin gona na wucin gadi 1,440 a ƙarƙashin shirinmu mai suna J-Agro. ” Inji Gwamnan.

A nasa jawabin shugaban hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar Jigawa, Farfesa Haruna Musa ya ce malaman da suka yi aikin koyarwa na wucin gadi na tsawon shekaru biyu a jihar an basu takardar aiki na dindindin  bayan cin jarrabawar da suka yi.

Ya ce, dukkanin malaman 3,143 an basu aikin ne bisa cancanta, ya kuma ba da tabbacin cewa, dukkansu suna da kwarewar da ta dace.

Farfesa Haruna Musa ya ce, hukumar za ta ci gaba da sanya ido kan sabbin ma’aikatan da aka dauka, kuma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen korar duk wanda ya kasa bin ka’idojin daukar ma’aikata.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara