Ilimi
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Takardar Kama Aiki Ga Malaman Makarantu Sama Da 3000
Gwamna Umar Namadi ya bayar da takardun kama aiki na dindindin ga malaman makarantu 3,143, tare da daukar ma’aikatan wucin gadi 2,445 a jihar.
Da yake jawabi a wajen bikin bayar da takardun kama aikin da aka gudanar a dakin taro na Malam Aminu Kano Triangle da ke Dutse, ya bayyana cewa, wannan gagarumin aikin na daga cikin tsare-tsare na samun nasarar aiwatar da manufofinsa guda 12.
Ya bayyana cewa babu wata manufa ta gwamnati da za a iya aiwatar da ita yadda ya dace ba tare da isasshen horo da kwararrun ma’aikata ba.

“Ajandarmu guda 12 da aka tsara don ganin jihar Jigawa ta bunkasa sun hada da samar da ilimi mai inganci ga daukacin yara a jihar, kuma don samun nasarar haka ya zama wajibi mu kara samar da kwararrun malamai.”
Ya ci gaba da bayanin cewa, a kokarin cimma burinsu na samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya ga daukacin ‘yan jihar, magance yawaitar mace-macen yara da mata masu juna biyu, samar da lafiyar al’umma da walwala, gwamnatin jihar ta tura dalibai sama da 120 zuwa kasashen Cyprus da Indiya domin karatun aikin likitanci.
A cewarsa, gwamnati mai ci ta kaddamar da gina makarantar koyon aikin jinya da ungozoma ta naira biliyan 5 da rabi, inda a yanzu ta bayar da aikin yi ga ma’aikatan lafiya 1,005 da suka hada da likitoci da kananan ma’aikata.
Gwamnan ya yi nuni da cewa, noma na daya daga cikin muhimman sassa na ajandarsa guda 12, wanda aka kudiri aniyar samar da ayyukan yi, kawar da fatara, samar da abinci, da kuma ci gaban tattalin arziki mai dorewa.

“Haɓaka amfani da fasahar noma ta zamani da samar da kayan aikin gona na zamani da araha ga manoma yana da matuƙar mahimmanci wajen cimma burin da aka sa a gaba, kuma bisa la’akari da hakan a yau muna gabatar da tayin aiki ga ma’aikatan aikin gona na wucin gadi 1,440 a ƙarƙashin shirinmu mai suna J-Agro. ” Inji Gwamnan.
A nasa jawabin shugaban hukumar kula da ilimin bai daya ta jihar Jigawa, Farfesa Haruna Musa ya ce malaman da suka yi aikin koyarwa na wucin gadi na tsawon shekaru biyu a jihar an basu takardar aiki na dindindin bayan cin jarrabawar da suka yi.
Ya ce, dukkanin malaman 3,143 an basu aikin ne bisa cancanta, ya kuma ba da tabbacin cewa, dukkansu suna da kwarewar da ta dace.
Farfesa Haruna Musa ya ce, hukumar za ta ci gaba da sanya ido kan sabbin ma’aikatan da aka dauka, kuma ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen korar duk wanda ya kasa bin ka’idojin daukar ma’aikata.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
