Connect with us

Ilimi

Gwamnan Jihar Kaduna Ya Ɗauki Nauyin Karatun Ɗaliban Kuriga

Published

on

Gwamna Uba Sani, na jihar Kaduna ya yi alkawarin bai wa ɗaliban Kuriga 137 da aka kubutar daga hannun ’yan bindiga tallafin karatu.

Uba Sani ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi ga daliban da suka kubuta daga hannun ‘yan bindiga a gidan gwamnatin jihar a ranar Alhamis.

Gwamnan ya ce gidauniyarsa ta Uba Sani za ta gyara makarantun Kuriga domin bai wa yara a garin damar samun ingantaccen ilimi.

Sani, ya Kara da cewar bayan sako daliban, gwamnatin jihar ta dauki masana ilimin halayyar dan adam aiki wadanda suka shafe lokaci suna tattaunawa da daliban don tabbatar da lafiyarsu.

Sai dai ya bayyana cewar ɗaya daga cikin malaman da aka sace, mai suna Malam Abubakar ya rasa ransa sakamakon matsalar rashin lafiya.

Gwamnan ya ce gwamnatin jihar za ta dauki nauyin karatun ’ya’yan malamin da ya rasu, tare da bai wa iyalansa kyautar Naira miliyan 10.

Sani ya ce, “Jiya iyayen daliban suka zo nan, sun hadu da yaran, kowa ya yi murna. Ina so na yaba wa yaran. Sun yi hakuri da mu. Sun kuma fahimci halin da suka tsinci kansu a ciki.

“Lokacin da suka dawo, mun fahimci wasu na cikin matsanancin hali. Wannan shi ne dalilin da ya sa muka dauko masana ilimin halayyar dan adam, wadanda suka ba su shawarwari. Na yi farin ciki kamar yadda yaran suka yi farin ciki.

“Kwana biyu da kubutarsu, sun nuna ba sa son komawa gida, sun so zama da ni a nan na tsawon mako biyu. Amma na sanar da su cewar ba zai yiwu ba dole su koma gida. Iyayensu na muradin ganin su bayan shafe kimanin kwana 17 a hannun ‘yan bindiga.”

Gwamnan ya kara da cewa, “Na kuma bayar da umarnin yin gyare-gyare a garin da kuma makarantunsu, domin Kuriga na daya daga cikin yankuna mafi zaman lafiya a Kaduna.”

 

Aminu Dalhatu

 

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara