Labarai
Gwamna Namadi Zai Biya Tallafin Naira Miliyan 1 Ga Kowani Mahajjaci
Gwamnan jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya amince da biyan tallafin Naira miliyan daya ga kowane mahajjaci daga jihar don yin aikin Hajjin bana a karkashin hukumar jin dadin alhazai ta jihar.
Shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.
A cewarsa, Gwamnan ya dauki matakin ne dangane da karin kudin Hajji da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta yi a baya-bayan nan wanda aka alakanta shi da rashin daidaiton farashin canji.
“Akwai mutanen da suka rigaya suka biya gaba daya, amma kwatsam sai aka samu karin kudin aikin Hajji, karin kudin aikin Hajji babban kalubale ne ga dimbin maniyyata.” Inji shi.

Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa Ahmad Umar Labo
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bukaci dukkan maniyyatan jihar da su tabbatar sun biya sauran kudaden da suka rage wato naira dubu dari tara da goma sha takwas ga hukumar.
Shugaban hukumar ya yi nuni da cewa wadanda za su ci gajiyar tallafin aikin Hajjin su ne wadanda dama sun biya kudin aikin Hajjin ga hukumar.
Idan dai za a iya tunawa, NAHCON ta sanar da karin kudin aikin Hajji da Naira miliyan daya da dubudaritaradagomashatakwas, wanda ya sa adadin kudin aikin Hajji ya kai naira miliyan shuda da dubu dari shida da goma sha bakwai.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
