Labarai
Gwamna Namadi Ya Nada Masu Bashi Shawara Na Musamman Su 5
Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya amince da nadin karin masu ba da shawara na musamman guda 5.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da sakataren gwamnatin jiha Malam Bala Ibrahim ya sanyawa hannu kuma ya mikawa manema labarai a Dutse.
Ya ce, wadanda aka nada sun hada da Abdulkadir Bala Umar T.O mai ba da shawara na musamman kan ayyuka na musamman, Uzairu Nadabo mai ba da shawara na musamman 2 EPZ da Ado Mai’unguwa mai ba da shawara na musamman kan kasuwanci.
Musa Shu’aibu Guri a matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin kudaden shiga yayin da Sa’idu Umar ya samu matsayin mai ba da shawara na musamman kan harkokin abinci.
Malam Bala Ibrahim ya bayyana cewa, anyi wannan nadin ne bias cancanta da cancanta.
“A yayin da nake taya sabbin mukaman da aka nada, ina kira gare ku da ku kasance masu gaskiya da adalci wajen sauke nauyin da aka dora muku, muna da babban aiki a gaban ku, kuma dukkan ku dole ne ku lura tare da aiki daidai da ajandar 12 na Gwamna Umar Namadi, domin gina jihar Jigawa.” in ji sakataren gwamnatin.
Bala Ibrahim ya kara da cewa, duk nade-naden ya fara aiki nan take.
KARSHE/USMAN MZ/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
