Labarai
Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Matasa Bisa Yada Manufofin Gwamnatin Jihar Jigawa
Gwamnan Jihar Jigawa Malam Umar Namadi ya kaddamar da taron yini biyu kan dandalin sada zumunta wanda cibiyar manema labarai ta Danmodi Media ta shirya.
Taron wanda ke gudana a cibiyar bunkasa ayyukan yi, ya tara matasa maza da mata daga kananan hukumomi 27 dake fadin jihar wadanda suke amfani da kafafen sadarwa na zamani.

A jawabinsa, Gwamna Umar Namadi ya jaddada jin dadinsa ga matasa da suke yada manufofin gwamnatin jihar Jigawa.
Ya gode musu bisa kokarinsu da jajircewarsu wajen kare muradun gwamnati.

“A madadina da duk wadanda suka tsaya takara a shekarar 2023, muna mika godiyarmu ga matasan kafafen sada zumunta na zamani bisa kokarinsu da jajircewarsu na samun nasara,” inji gwamnan.
Namadi ya kuma gargadi matasa da su guji yin amfani da su da kuma yada abubuwan da ba su dace ba da ka iya keta mutuncin mutane.

Ya yaba da irin gudunmawar da matasan suka bayar wajen samun nasarar gwamnati tare da ba su tabbacin karrama su busa wannan kokari da suke yi.
Gwamna Namadi ya kuma mika godiyarsa ga wadanda suka shirya taron na wayar da kan matasa kan yadda ake amfani da kafafen sadarwa na zamani.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
