Connect with us

Labarai

Gwamna Bago Ya Bayyana Gamsuwarsa Game Da Aikin Gyaran Asibitin IBB

Published

on

Gwamnan jihar Neja, Mohammed Umar Bago, ya bayyana gamsuwarsa da aikin sake fasalin Asibitin Kwararru na IBB da ke Minna.

Gwamnan ya bayyana haka ne bayan ya duba aikin fadada asibitin da ake yi, inda ya yaba wa ‘yan kwangilar da ke gudanar da aikin bisa inganci.

Umar Bago ya yi amfani da wannan dama wajen jaddada kudirin gwamnatinsa na farfado da bangaren kiwon lafiya, domin bai wa al’ummar jihar Neja damar samun ingantacciyar kulawa.

Tun da farko, gwamnan ya ayyana dokar ta baci a fannin lafiya, inda aka fara tsauraran gyare-gyare, sake ginawa da kuma sabunta cibiyoyin kiwon lafiya a sassan jihar.

Ana cigaba da gyare-gyare a Asibitin Kwararru na IBB da ke Minna, inda aka kammala sabunta bangarori kamar na gaggawa (Emergency/Accident Unit), Sashen Majinyata na Gabaɗaya (General Outpatients Department), Sashen Kulawa na Musamman (ICU), ofisoshin likitoci da Nas Nas, da kuma sashen gadajen majinyata na musamman (VIP Units), tare da samar da kayayyakin zamani na lafiya.

Bayan haka, an gina gidajen likitoci guda biyu masu dakuna biyu kowanne, da kuma tankin ruwa mai daukar lita 42,000 a sama, da ƙara gina rijiyar burtsatse.

Haka kuma, an samar da na’urar Elizer da ke duba jinin ɗan adam, tare da sabon janareta mai ƙarfin KV 100 domin cibiyar gwaje-gwaje ta NNPC, da kuma janareta mai ƙarfin 300 KVA, tare da wasu na’urori da ake amfani da su a asibitin.

Daga Aliyu Lawal

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara