Connect with us

Ilimi

Gidauniyar IRM ta Bada Tallafin Guraben Karatu ga Daliban Kiwon Lafiya 100 a Kaduna

Published

on

 

Daga Abdullahi Shettima

Gidauniyar IRM ta bayar da guraben karatu ga dalibai 100 na fannin Community Health, domin ƙarfafa ma’aikatan lafiya da inganta samun kulawar asali a yankunan da ba su da wadatattun hidimomi.

An gudanar da bikin bayar da guraben ne a yayin yaye dalibai na Aisha Ameer Healthcare Institute da ke Rigasa a Jihar Kaduna, inda iyaye, shugabanni na al’umma da jami’an ilimi suka hallara domin shaida wannan gagarumar gudunmawa.

Mai wakiltar Gidauniyar IRM, Alhaji Baba Sidi Kabir Mohammed, ya ce an kaddamar da shirin ne don tallafa wa matasa masu kishin aikin lafiya amma ke fuskantar ƙalubalen kuɗi da kan hana su ci gaba da karatu. Ya jaddada cewa gidauniyar ta daɗe tana mayar da hankali kan habaka jigon ɗan Adam, musamman a sashen kiwon lafiya.

A cewar gidauniyar, an zaɓi waɗanda suka ci gajiyar shirin ne bayan tantancewa bisa bajinta da kuma aniyar su ta mayar wa al’umma da ilimin da za su samu. Tallafin ya rufe kuɗin makaranta gaba ɗaya domin bai wa dalibai damar nutsuwa a karatunsu.

Mai magana da yawun gidauniyar ya ce, “Tallafa wa waɗannan matasa tamkar inganta rayuwar al’umma gaba ɗaya ne. Idan aka ba ɗalibai damar da suke nema, suna dawowa su yi aiki da jajircewa da gaskiya. Wannan shi ne hangen nesa na Gidauniyar IRM.”

Daraktan Aisha Ameer Healthcare Institute, Dr. Yahaya Balarabe, ya yabawa gidauniyar bisa wannan aiki na alheri tare da jinjina wa Wanda ya kafa ta, Hon. Ibrahim Rilwan Muhammad, bisa jajircewa wajen tallafa wa fannin lafiya da samar da ƙwararrun ma’aikata da za su yi aiki a matakai daban-daban na al’umma.

Haka nan, Hakimin Rigasa, Arc. Mohammed Aminu Idris, ya gode wa Gidauniyar IRM da mai kafawa bisa zaɓar Rigasa cikin yankunan da suka ci gajiyar shirin. Ya ce gudunmawar za ta taimaka ƙwarai wajen bunƙasa kula da lafiyar jama’a, musamman a unguwanni masu buƙatar ƙarin ma’aikata.

Daga cikin waɗanda suka ci gajiyar guraben, Fatima Abdul Salam, ta bayyana godiya a madadin sauran dalibai, inda ta ce tallafin ya rage wa iyalai nauyin da ya daɗe yana damunsu. Ta gode wa Hon. Ibrahim Rilwan Muhammad bisa ƙoƙarin da ya yi na buɗe wa matasa sabuwar hanya ta samun ilimi da cigaba.

Masu ruwa da tsaki a fannin lafiya sun yaba da wannan mataki, suna mai kira ga sauran kungiyoyi da masu hannu da shuni da su yi koyi da Gidauniyar IRM domin inganta kiwon lafiya a ƙasar nan.

Ana sa ran tallafin zai ƙara yawan ƙwararrun ma’aikatan Community Health da za su shiga aiki, abin da zai inganta ayyukan kiwon lafiya a matakin ƙauyuka da unguwanni.

 

Labarai

Labarai37 minutes ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Aikin Ban-ruwa

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai20 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara