Ilimi
Gidauniyar IRM ta Bada Tallafin Guraben Karatu ga Daliban Kiwon Lafiya 100 a Kaduna
Daga Abdullahi Shettima
Gidauniyar IRM ta bayar da guraben karatu ga dalibai 100 na fannin Community Health, domin ƙarfafa ma’aikatan lafiya da inganta samun kulawar asali a yankunan da ba su da wadatattun hidimomi.
An gudanar da bikin bayar da guraben ne a yayin yaye dalibai na Aisha Ameer Healthcare Institute da ke Rigasa a Jihar Kaduna, inda iyaye, shugabanni na al’umma da jami’an ilimi suka hallara domin shaida wannan gagarumar gudunmawa.
Mai wakiltar Gidauniyar IRM, Alhaji Baba Sidi Kabir Mohammed, ya ce an kaddamar da shirin ne don tallafa wa matasa masu kishin aikin lafiya amma ke fuskantar ƙalubalen kuɗi da kan hana su ci gaba da karatu. Ya jaddada cewa gidauniyar ta daɗe tana mayar da hankali kan habaka jigon ɗan Adam, musamman a sashen kiwon lafiya.
A cewar gidauniyar, an zaɓi waɗanda suka ci gajiyar shirin ne bayan tantancewa bisa bajinta da kuma aniyar su ta mayar wa al’umma da ilimin da za su samu. Tallafin ya rufe kuɗin makaranta gaba ɗaya domin bai wa dalibai damar nutsuwa a karatunsu.
Mai magana da yawun gidauniyar ya ce, “Tallafa wa waɗannan matasa tamkar inganta rayuwar al’umma gaba ɗaya ne. Idan aka ba ɗalibai damar da suke nema, suna dawowa su yi aiki da jajircewa da gaskiya. Wannan shi ne hangen nesa na Gidauniyar IRM.”
Daraktan Aisha Ameer Healthcare Institute, Dr. Yahaya Balarabe, ya yabawa gidauniyar bisa wannan aiki na alheri tare da jinjina wa Wanda ya kafa ta, Hon. Ibrahim Rilwan Muhammad, bisa jajircewa wajen tallafa wa fannin lafiya da samar da ƙwararrun ma’aikata da za su yi aiki a matakai daban-daban na al’umma.

Haka nan, Hakimin Rigasa, Arc. Mohammed Aminu Idris, ya gode wa Gidauniyar IRM da mai kafawa bisa zaɓar Rigasa cikin yankunan da suka ci gajiyar shirin. Ya ce gudunmawar za ta taimaka ƙwarai wajen bunƙasa kula da lafiyar jama’a, musamman a unguwanni masu buƙatar ƙarin ma’aikata.
Daga cikin waɗanda suka ci gajiyar guraben, Fatima Abdul Salam, ta bayyana godiya a madadin sauran dalibai, inda ta ce tallafin ya rage wa iyalai nauyin da ya daɗe yana damunsu. Ta gode wa Hon. Ibrahim Rilwan Muhammad bisa ƙoƙarin da ya yi na buɗe wa matasa sabuwar hanya ta samun ilimi da cigaba.
Masu ruwa da tsaki a fannin lafiya sun yaba da wannan mataki, suna mai kira ga sauran kungiyoyi da masu hannu da shuni da su yi koyi da Gidauniyar IRM domin inganta kiwon lafiya a ƙasar nan.
Ana sa ran tallafin zai ƙara yawan ƙwararrun ma’aikatan Community Health da za su shiga aiki, abin da zai inganta ayyukan kiwon lafiya a matakin ƙauyuka da unguwanni.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
