Ilimi
Farfesa Tukur Adamu Ya Fara Aiki a Matsayin Shugaban Jami’ar Tarayya Gusau na Hudu
Daga Aminu Dalhatu
Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya ta Gusau (FUGUS) Farfesa Tukur Adamu ya yi alƙawarin inganta ilimi, bincike, ƙirƙire-ƙirƙire, walwalar ɗalibai da ma’aikata.
Farfesa Tukur Adamu wanda ya gaji Professor Mu’azu Gusau Abubakar bayan kammala wa’adinsa na shekaru biyar, ya bayyana hakan ne yayin da ya karɓi ragamar shugabancin Jami’ar a matsayin shugabata na huɗu.
Sabon Shugaban ya ce zai mayar da hankali kan binciken da zai magance matsalolin al’umma, kamar yadda ya yi a UDUS.
Ya kuma yi alƙawarin haɗa kai da gwamnatin Zamfara, Sarakuna, Jami’an tsaro da ƙungiyoyin addini domin ci gaban jami’ar.
An naɗa shi ne a taron Majalisar Gudanarwar jami’ar a watan Disamba 2025.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
