Connect with us

Ilimi

Farfesa Gumel Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Tarayya Da Ke Dutse

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Majalisar Gudanarwa ta huɗu ta Jami’ar Tarayya da ke Dutse (FUD) a Jihar Jigawa ta amince da naɗa Farfesa Ahmed Muhammed Gumel a matsayin shugabar jami’ar na huɗu.

Shugaban Majalisar Gudanarwar jami’ar, Farfesa Shuaibu Oba Abdulraheem, ya bayyana cewa an bi tsari mai tsauri da cikakken bincike wajen zaɓen sabon shugaban jami’ar.

A cewarsa, an tantance ’yan takara 2, inda a ƙarshe Farfesa Gumel ya fito a matsayin sabon Shugaban Jami’ar ta FUD.

Farfesa Uba ya taya sabon shugaban jami’ar murna,  tare da yi masa fatan Allah Ya mishi jagora da nasara wajen sauke nauyin da aka dora masa.

A nasa jawabin, sabon Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Ahmad Muhammad Gumel, ya gode wa Allah Madaukakin Sarki bisa zaɓensa a matsayin sabon shugaban jami’ar.

Ya kuma miƙa godiyarsa ga kwamitin haɗin gwiwar zaɓe, Shugaban Majalisar Gudanarwa, shugaban jami’ar mai ci, da dukkan mambobin majalisar jami’ar bisa amincewa da suka nuna masa.

Ya ƙara da cewa zai yi iya ƙoƙarinsa wajen ci gaba da gina nasarorin da shugaban jami’ar mai barin gadi ya samar.

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa Farfesa Ahmad Mohammed Gumel tsohon ɗalibi ne na Jami’ar Malaya da ke ƙasar Malaysia, inda ya samu digiri na biyu (Master) a fannin Kimiyyar Halittu ta Biotechnology da kuma digiri na uku (Ph.D) a Industrial Biotechnology, tare da ƙwarewa a Biocatalysis da Bioprocess.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara