Ilimi
Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN
Babbar Mai Shari’ar ta kasa , Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta jaddada cewa alkalai suna da nauyin tabbatar da adalci cikin gaskiya da daidaito a lokacin da matsalolin tattalin arziki ke kara tsananta wa al’umma.
Ta bayyana haka ne a Taron Alkalai na Shekara-shekara Karo na 26, wanda Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta shirya tare da haɗin gwiwar Cibiyar Koyar da Ayyukan Shari’a ta Kasa (NJI), a harabar Jami’ar da ke Kongo, Zariya.
Mai Shari’a Kekere-Ekun, wadda Sakatare na NJI, Barista Abdulazeez Aluwo ya wakilta, ta ce dole ne kotuna su yi hukunci da ke la’akari da yanayin tattalin arziki da kuma hakkokin masu nema da wadanda ake binsu hukunci.
Ta ce hakan ne kadai zai tabbatar da zaman lafiya da daidaiton al’umma.

Barista Abdulazeez Aluwo
CJN ta yi nuni da cewa rikice-rikicen harkokin kuɗi na zamani kamar hauhawar farashi da faduwar darajar naira, da canjin musayar kuɗi suna buƙatar tsantsar fassarar hukunce-hukuncen Shari’a bisa ilimi na zamani.
Ta yi kira da a kafa Kwamitin Tuntuba da zai kunshi Alkalai na kotu daukaka kara da Khadi da Manyan malamai na Shari’a da Kwararru a fannin kuɗi na zamani.
A cewarta, wannan kwamiti zai taimaka wajen ba kotuna jagoranci kan sabbin al’amuran da ke tasowa, tare da wayar da kan jama’a a kan dokokin kuɗin Shari’a.
Tun da farko, Daraktan Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci, Dakta. Sa’ad Abubakar, ya ce faduwar darajar kuɗi da hauhawar farashi suna barazana ga mu’amalar kasuwanci da aiwatar da shari’a.
Ya ce wannan al’amari na kara jefa kotunan Shari’a cikin matsaloli, musamman wajen tabbatar da adalci kan batutuwa masu alaƙa da mu’amaloli.
A sakonsa Mai martaba, Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli wanda Wazirin Zazzau Khadi Muhammad Inuwa Aminu ya wakilta, ya bukaci a hanzarta gyare-gyare a fannin Shari’a, musamman saboda yadda matsalar tattalin arziki ke shafar shari’o’in hul’i, da sadaki da dai sauransu.
Ana Shi bangare, Shugaban NJI, Mai Shari’a Babatunde Adejumo wanda Barista Zainab Salim ta wakilta ya yabawa sabon MOU da aka kulla tsakaninsu da ABU a fannin horaswa da bincike, da jagoranci da kuma inganta cancanta.
Ya ce taken taron na bana ya dace matuka, domin ya shafi manyan hakkoki na Shari’a kamar bashi da gado da sadaki, da mu’amaloli na yau da kullum.

Da yake Jawabi, Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Adamu Ahmad, Wanda Mataimakinsa a fannin Sha’anin Mulki Farfesa Suleiman Sabo ya wakilta ya ce taron alkalai na shekara–shekara muhimmin mataki ne da ke zurfafa tattaunawar shari’a da bunkasa bincike a fannin Shari’a a Najeriya.
A jawabinsa, tsohon Daraktan Cibiyar, Farfesa Muhammad Bello Usman, ya jaddada cewa adalci ba zai samu ba sai an dora nauyi da alhaki a kan mutanen da suka cancanta da kwarewa.
Taken Taron Shi ne : Shari’a a Yanayin Tattalin Arzikin Zamani: Tasirin Darajar Kuɗi da Canjin Musayar Kuɗi a Kan dokokin Shari’a.
Daga Ibrahim Suleiman
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
