Connect with us

Ilimi

Faduwar Darajar Kuɗi Na Kara Tsananta Kalubale Ga Kotunan Shari’a — CJN

Published

on

Babbar Mai Shari’ar ta kasa , Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun, ta jaddada cewa alkalai suna da nauyin tabbatar da adalci cikin gaskiya da daidaito a lokacin da matsalolin tattalin arziki ke kara tsananta wa al’umma.

Ta bayyana haka ne a Taron Alkalai na Shekara-shekara Karo na 26, wanda Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci ta Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta shirya tare da haɗin gwiwar Cibiyar Koyar da Ayyukan Shari’a ta Kasa (NJI), a harabar Jami’ar da ke Kongo, Zariya.

Mai Shari’a Kekere-Ekun, wadda Sakatare na NJI, Barista Abdulazeez Aluwo ya wakilta, ta ce dole ne kotuna su yi hukunci da ke la’akari da yanayin tattalin arziki da kuma hakkokin masu nema da wadanda ake binsu hukunci.

Ta ce hakan ne kadai zai tabbatar da zaman lafiya da daidaiton al’umma.

Barista Abdulazeez Aluwo

CJN ta yi nuni da cewa rikice-rikicen harkokin kuɗi na zamani kamar hauhawar farashi da faduwar darajar naira, da canjin musayar kuɗi suna buƙatar tsantsar fassarar hukunce-hukuncen Shari’a bisa ilimi na zamani.

Ta yi kira da a kafa Kwamitin Tuntuba da zai kunshi Alkalai na kotu daukaka kara da Khadi da Manyan malamai na Shari’a da Kwararru a fannin kuɗi na zamani.

A cewarta, wannan kwamiti zai taimaka wajen ba kotuna jagoranci kan sabbin al’amuran da ke tasowa, tare da wayar da kan jama’a a kan dokokin kuɗin Shari’a.

Tun da farko, Daraktan Cibiyar Nazarin Shari’ar Musulunci, Dakta. Sa’ad Abubakar, ya ce faduwar darajar kuɗi da hauhawar farashi suna barazana ga mu’amalar kasuwanci da aiwatar da shari’a.

Ya ce wannan al’amari na kara jefa kotunan Shari’a cikin matsaloli, musamman wajen tabbatar da adalci kan batutuwa masu alaƙa da mu’amaloli.

A sakonsa Mai martaba, Sarkin Zazzau, Mal. Ahmed Nuhu Bamalli wanda Wazirin Zazzau Khadi Muhammad Inuwa Aminu ya wakilta, ya bukaci a hanzarta gyare-gyare a fannin Shari’a, musamman saboda yadda matsalar tattalin arziki ke shafar shari’o’in hul’i, da sadaki da dai sauransu.

Ana Shi bangare, Shugaban NJI, Mai Shari’a Babatunde Adejumo wanda Barista Zainab Salim ta wakilta ya yabawa sabon MOU da aka kulla tsakaninsu da ABU a fannin horaswa da bincike, da jagoranci da kuma inganta cancanta.

Ya ce taken taron na bana ya dace matuka, domin ya shafi manyan hakkoki na Shari’a kamar bashi da gado da sadaki, da mu’amaloli na yau da kullum.

Da yake Jawabi, Shugaban Jami’ar Ahmadu Bello, Farfesa Adamu Ahmad, Wanda Mataimakinsa a fannin Sha’anin Mulki Farfesa Suleiman Sabo ya wakilta ya ce taron alkalai na shekara–shekara muhimmin mataki ne da ke zurfafa tattaunawar shari’a da bunkasa bincike a fannin Shari’a a Najeriya.

A jawabinsa, tsohon Daraktan Cibiyar, Farfesa Muhammad Bello Usman, ya jaddada cewa adalci ba zai samu ba sai an dora nauyi da alhaki a kan mutanen da suka cancanta da kwarewa.

Taken Taron Shi ne : Shari’a a Yanayin Tattalin Arzikin Zamani: Tasirin Darajar Kuɗi da Canjin Musayar Kuɗi a Kan dokokin Shari’a.

Daga Ibrahim Suleiman 

Labarai

Labarai40 minutes ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai20 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara