Connect with us

Kasuwanci

Daliban BUK 300 Za Su Ci Gajiyar Horon Aikin Gona don Kasuwanci

Published

on

Cibiyar Noma a Yankunan Busassu (Centre for Dryland Agriculture – CDA) ta Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta haɗa gwiwa da Ƙungiyar Ci Gaban Mata Manoma (Women Farmers Advancement Network – WOFAN) da kuma Kwalejin Aikin Gona, domin horas da daliban aikin gona 300 a duk shekara kan harkokin noma don kasuwanci da ƙara darajar amfanin gona, sarrafawa da kuma samarwa, ƙarƙashin shirin SIBLING Project.

Shirin, wanda ya shafi daliban matakai na aji 3 zuwa 4, an bayyana shi ne yayin wata ziyarar girmamawa da tawaga ta haɗin gwiwa daga WOFAN, CDA da Kwalejin Aikin Gona suka kai wa Shugaban Jami’ar, Farfesa Haruna Musa.

A ƙarƙashin shirin, CDA ta ware filin gwaji mai girman hekta biyu, yayin da Kwalejin Aikin Gona ta samar da hekta 25 domin noman manyan gonaki da horo na aikace-aikace.

Shirin zai kuma bai wa dalibai damar fahimtar darajar noma da kasuwancin noma da kwarewar aikace-aikace da ke taimakawa bunƙasa aiki mai ɗorewa.

Da yake jawabi a lokacin ziyarar, Farfesa Haruna Musa ya yaba da haɗin gwiwar, inda ya bayyana ta a matsayin muhimmin tsari na ƙarfafa matasa da mata, yana mai nuna cewa mata 180 ne daga cikin daliban 300 da za su amfana da shirin.

Da yake karin haske kan haɗin gwiwar, Daraktan CDA, Farfesa Sanusi Gaya Mohammed, ya bayyana cewa CDA da WOFAN sun samu damar amfani da rumbun ajiya na ƙasa ta hannun Cibiyar Ƙasa ta Inganta Ayyukan Rumbunan Ajiya ta Nijeriya (National Storage Productivity Institute of Nigeria).

A nata jawabin, Daraktar WOFAN a ƙasa, Dakta Salamatu Garba, ta ce shirin na da nufin sauya yadda mata da matasa ke shiga harkar noma ta hanyar basu kwarewa, samun filayen noma da kayan aiki, tare da kasuwa mai tabbas.

Shi ma yana jawabi, Dekan Kwalejin Aikin Gona, Farfesa Muhammad Auwal Hussain, ya ce shirin ya samo asali ne daga buƙatun dalibai da matan ma’aikata, tare da haɗa al’ummomi biyu daga yankin Zango domin ƙarfafa hulɗar al’umma da ci gaba mai haɗa kowa da kowa.

Khadijah Aliyu

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara