Connect with us

Labarai

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Published

on

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta amince da ita kwanan nan.

Ƙungiyar ta yi gargaɗin cewa kudirin dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar ta gabatar na nuna wariya da nuna bambanci ga Kiristoci a jihar.

Shugaban CAN na jihar, Mai Girma Uba (Most Reverend) Bulus Dauwa Yohanna, ya bayyana matsayar ƙungiyar a cikin wata sanarwa da aka bai wa ’yan jarida a Minna. Ya nuna damuwa cewa kudirin Niger State Hisbah Directorates Bill, wanda ɗan majalisa mai wakiltar mazaɓar Chanchaga, Mohammed Abubakar, ya gabatar, kudiri ne mai cike da cece-kuce wanda bai kamata Gwamnan jihar, Umar Bago, ya sanya wa hannu ya zama doka ba.

Wani ɓangare na sanarwar Shugaban ya ce:
“Gwamna Mohammed Umar Bago, mu dukkan Kiristoci a jihar nan muna jan hankalinka kan wani abu da zai iya haifar da rarrabuwar kawuna a tsakanin al’ummar da kake jagoranta, kuma muna roƙonka da kada ka sanya wa wannan kudiri hannu ya zama doka.”

Shugaban CAN, wanda kuma shi ne Bishop na Katolika na Diocese na Kontagora, ya tambaya da cewa: “Me ya sa dokar Hisbah a Jihar Niger? Mene ne manufarta? Wane amfani za ta kawo wa al’ummarmu ta fuskar tattalin arziki da zamantakewa? Shin ’yan majalisar sun fahimci cewa Kiristoci ba za su kasance ƙarƙashin dokar Hisbah ba?”

Bishop Bulus Yohanna ya ba da shawarar cewa akwai rundunar ’yan sandan Nijeriya, Hukumar Tsaron Fararen Hula (NSCDC), kungiyoyin sa-kai (Vigilante) da sauran hukumomi da ƙungiyoyi da kundin tsarin mulki ya ba su ikon aiki. Ya kuma yi kira ga dukkan al’ummar Jihar Niger masu kishin ƙasa—ba tare da la’akari da addini, kabila ko ra’ayin siyasa ba—da su haɗa murya domin tabbatar da cewa kudirin bai zama doka ba.

PR Aliyu Lawal

 

 

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara