Labarai
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba
Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a Jihar Taraba.
Wannan babbar hanya mai yawan zirga-zirga, wadda ke haɗa jihar da yankunan kudancin Nijeriya, na cikin Ƙaramar Hukumar Gassol a jihar.
Abin tunawa ne cewa ambaliyar ruwa ta shekarar 2024 ce ta wanke gadar, lamarin da ya katse muhimmin hanyar sufuri tare da jefa masu amfani da hanya cikin wahala. Haka kuma, a sakamakon rushewar gadar a shekarun baya, an rasa rayuka da dama bayan aukuwar haɗurran jiragen ruwa (ƙananan kwale-kwale).
A halin da ake ciki, wata babbar tawaga daga NEDC, wadda ta ziyarci Jihar Taraba a ƙarshen mako domin ƙaddamar da ayyukan da ta aiwatar a faɗin jihar, ta kai ziyara wurin gadar domin duba yadda aikin ke tafiya.
Tawagar ta samu jagorancin Ministan Ƙananan Harkokin Raya Yankuna, wanda kuma ɗan asalin jihar ne, Hon. Uba Maigari Ahmadu. A cikin tawagar akwai Shugaban Kwamitin Gudanarwa na NEDC, Manjo Janar Paul Tarfa; Darakta Janar/ Shugaban Zartarwa na Hukumar, Mohammed Goni Alkali; ’yan Majalisar Dokoki ta Ƙasa; Daraktocin Zartarwa; mambobin Kwamitin Gudanarwa; da manyan jami’an gudanarwa na hukumar.
Da yake magana da ’yan jarida, Ministan ya ce ziyarar duba aikin na da nufin tantance ci gaba, ganin cewa tuni aka tura ’yan kwangila domin kammala aikin cikin gaggawa, don rage wa masu amfani da hanyar wahalhalu.
Hon. Uba Maigari Ahmadu ya bayyana cewa sake gina gadar da sauran ayyuka masu yawa da NEDC ta aiwatar a faɗin Jihar Taraba sun yi daidai da Manufar “Renewed Hope” ta Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.
Ministan ya nuna farin ciki da fara aikin gadar a ƙarshe, tare da jaddada ƙudurin Shugaba Tinubu na samar da romon dimokuraɗiyya ga yankin da ƙasar nan baki ɗaya.
A nasa ɓangaren, Darakta Janar na NEDC, Mohammed Goni Alkali, ya bayyana tsoma-bakin a matsayin abin da ya zama dole domin rage wahalhalun da rushewar gadar ta haifar da kuma farfaɗo da harkokin tattalin arziki a yankin.
Ya sake tabbatar da jajircewar hukumar wajen hanzarta aiwatar da ayyukan raya kasa a yankin Arewa maso Gabas.
Wasu ’yan Nijeriya da ke yawan bin wannan hanya, a zantawarsu da wakilinmu, sun bayyana farin cikinsu da fara aikin ginin gadar, tare da yaba wa NEDC bisa cika aikinta.
Sani Sulaiman
-
Labarai6 days agoRamadan: Sarkin Kauru Ya Bukaci a Kara Karfafa Tsaro Tare da Tallafawa Marasa Galihu
-
Labarai5 days agoKaramar Hukumar Birnin Kudu ta Nemi Hadin Kan Kungiyar ‘Yan Achaba Wajen Dakile Matsalar Tsaro
-
Labarai5 days agoSojojin Najeriya Sun Karɓi Motocin Yakin Da Aka Kera A Cikin Ƙasa
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kano Ta Fara Shari’ar Tsige Mataimakin Gwamna Aminu Abdulsalam
-
Labarai2 days agoRanar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata
-
Labarai5 days agoTsarin Kundin Shirin Bunkasa Samarda Abinci Mai Gina Jiki
-
Labarai6 days agoKungiyoyin Alumma a Jigawa Sun Bayyana Goyon Bayansu ga Gwamna Namadi Kan Lamarin Walida Abdulhadi
-
Labarai4 days agoGwamnatin Zamfara Ta Ayana Dokar Ta-baci Kan Shan-Inna a Karamar Hukumar Gummi
