Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Published

on

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a Jihar Taraba.

Wannan babbar hanya mai yawan zirga-zirga, wadda ke haɗa jihar da yankunan kudancin Nijeriya, na cikin Ƙaramar Hukumar Gassol a jihar.

Abin tunawa ne cewa ambaliyar ruwa ta shekarar 2024 ce ta wanke gadar, lamarin da ya katse muhimmin hanyar sufuri tare da jefa masu amfani da hanya cikin wahala. Haka kuma, a sakamakon rushewar gadar a shekarun baya, an rasa rayuka da dama bayan aukuwar haɗurran jiragen ruwa (ƙananan kwale-kwale).

A halin da ake ciki, wata babbar tawaga daga NEDC, wadda ta ziyarci Jihar Taraba a ƙarshen mako domin ƙaddamar da ayyukan da ta aiwatar a faɗin jihar, ta kai ziyara wurin gadar domin duba yadda aikin ke tafiya.

Tawagar ta samu jagorancin Ministan Ƙananan Harkokin Raya Yankuna, wanda kuma ɗan asalin jihar ne, Hon. Uba Maigari Ahmadu. A cikin tawagar akwai Shugaban Kwamitin Gudanarwa na NEDC, Manjo Janar Paul Tarfa; Darakta Janar/ Shugaban Zartarwa na Hukumar, Mohammed Goni Alkali; ’yan Majalisar Dokoki ta Ƙasa; Daraktocin Zartarwa; mambobin Kwamitin Gudanarwa; da manyan jami’an gudanarwa na hukumar.

Da yake magana da ’yan jarida, Ministan ya ce ziyarar duba aikin na da nufin tantance ci gaba, ganin cewa tuni aka tura ’yan kwangila domin kammala aikin cikin gaggawa, don rage wa masu amfani da hanyar wahalhalu.

Hon. Uba Maigari Ahmadu ya bayyana cewa sake gina gadar da sauran ayyuka masu yawa da NEDC ta aiwatar a faɗin Jihar Taraba sun yi daidai da Manufar “Renewed Hope” ta Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu.

Ministan ya nuna farin ciki da fara aikin gadar a ƙarshe, tare da jaddada ƙudurin Shugaba Tinubu na samar da romon dimokuraɗiyya ga yankin da ƙasar nan baki ɗaya.

A nasa ɓangaren, Darakta Janar na NEDC, Mohammed Goni Alkali, ya bayyana tsoma-bakin a matsayin abin da ya zama dole domin rage wahalhalun da rushewar gadar ta haifar da kuma farfaɗo da harkokin tattalin arziki a yankin.

Ya sake tabbatar da jajircewar hukumar wajen hanzarta aiwatar da ayyukan raya kasa a yankin Arewa maso Gabas.

Wasu ’yan Nijeriya da ke yawan bin wannan hanya, a zantawarsu da wakilinmu, sun bayyana farin cikinsu da fara aikin ginin gadar, tare da yaba wa NEDC bisa cika aikinta.

Sani Sulaiman

Labarai

Labarai18 hours ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai2 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Ilimi2 days ago

Hukumar Ilimantar Da Makiyaya Ta Kasa Ta Horarda Ma’aikatanta Kan Yanda Za’a Mayarda ‘Ya’yan Makiyaya Makaranta 

  By Adamu Yusuf   Hukumar Ilimantar da Makiyaya Ta Kasa (NCNE) ta shirya taron horas da ma’aikatan ta kan...

Labarai2 days ago

NCAA ta Yaba wa Hukumar Alhazai ta Jihar Kebbi Bisa Kyakkyawan Tanadin Aikin Hajji

Daga Sani Dutsinma Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Najeriya (NCAA), ta yaba da kokarin Hukumar Jin Daɗin Alhazai...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Kashe ’Yan Bindiga 45 a Katsina

Rundunar sojin Najeriya ta kashe ’yan bindiga 45 a wani mummunan artabu da aka yi a yankin Danmusa na cikin...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Ta Bukaci Malamai Su Yi Wa’azin Zaman Lafiya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta karyata zargin cewa gwamnatin Gwamna Nasir Idris ba ta taka rawar gani wajen bunkasa harkokin addinin...

Labarai2 days ago

Ranar Mata Ta Duniya: Gwamnatin Kano Ta Bukaci A Kara Tallafa wa Mata da ’Yan Mata

Kwamishinar Harkokin Mata, Yara da Masu Bukata ta Musamman ta Jihar Kano, Amina Abdullahi, ta bukaci masu ruwa da tsaki...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yi Kira Da A Karfafa Mata

Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta bukaci hukumomin gwamnati, abokan hulda na ci gaba, sarakuna, malamai da...

Labarai2 days ago

’Yan Sanda Sun Kama Mutane Biyu Kan Lalata Kayan Wutar Lantarki a Nasarawa

Rundunar ’yan sandan Jihar Nasarawa ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da lalata igiyoyi da sandunan wutar lantarki...

Labarai2 days ago

NSCDC Ta Kama Mutane Biyu Da Ake Zargin ’Yan Bindiga Ne a Kwara

Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya NSCDC a Jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargi da alaka...

Mafi Shahara