Connect with us

Labarai

Bauchi ta kafa kwamitin Limamai da Fastoci don tabbatar da zaman lafiya a Tafawa Balewa da Bogoro

Published

on

Gwamnatin jihar Bauchi ta kaddamar da wani kwamiti na musamman na Limamai da Fastoci domin samar da hadin kai da zaman lafiya a kananan hukumomin Tafawa Balewa da Bogoro bayan wani rikici da ya barke a yanki  kwanakin baya.

Gwamnan jihar Bala Muhammad a lokacin da yake kaddamar da kwamitin a gidan gwamnati da ke Bauchi ya ce bai zai yi kasa a qwiwa ba wajen daukan matakan da su ka da ce don magance barazanar bata gari da ke kokarin wargaza zaman lafiya da tsaro a yankunan.

Bala Muhammad ya ce zaman lafiya shine ginshikin kashin bayan kowace al’umma don haka akwai bukatar a hada  malaman addini musamman Limamai da Fastoci don su suka fi kusa da Al’ummah da kuma dimbin mabiya domin wayar da kan mabiyansu kan zaman lafiya da kuma zimmar dakile sa ke barkewar rikici a kananan hukumomin biyu.

Gwamnan ya bukaci mambobin kwamitin da su yi aiki tare da masu ruwa da tsaki daban-daban don tabbatar da dorewar zaman lafiya da aka samu a kananan hukumomin biyu cikin shekaru da dama da suka gabata wanda a yanzu aka samu tsaiko  sakamakon rikicin manoma da makiyaya da ya yi sanadin asarar rayuka da dukiyoyi.

Ya bukace su da su kai rahotonin duk wani abu da su ke zargi da ya wuce ikon su ga hukumomin tsaro da abin ya shafa domin daukar matakin gaggawa.

“Ba za mu bari wani ya lalata zaman lafiyar da muka gina ba,” in ji Gwamnan. “Wannan kwamitin zai zama gada tsakanin al’umma, domin samar da fahimtar juna da zaman lafiya.”

Gwamnan ya yi bayanin ayyukan kwamitin da su ka hada da wayar da kan jama’a kan samar da zaman lafiya da tattaunawa da yin sulhu a tsakanin jama’a da nufin haka ta cimma ruwa.

Da suke mayar da martani a madadin kwamatin, Shuwagabanin kwamitin Faizu Ado Musa daga karamar hukumar Tafawa Balewa da Reverend Father Benson Bature daga karamar hukumar Bogoro sun yi alkawarin yin aiki tukuru har sai an dawo da zaman lafiya mai dorewa a yankunan.

“Za mu yi duk mai yiwa wajen sake nauyin da aka dora mana da taimakon Allah. Kuma in Allah yarda duk wadda ya ke da hannu wajen tayar da rikici a yankunanmu Allah ba zai bar shi ba”.

Shugabannin hukumomin tsaro daban-daban da suka hada da kwamishinan ‘yan sandan jihar, daraktan tsaro na jiha.  Kwamandojin soji na sama da kasa da sauransu na daga cikin waya’nda su ka halarci taron.

Cov/Alhassan.

Labarai

Labarai9 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi9 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai10 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai11 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara