Connect with us

Labarai

Ana binciken gano waɗanda suka ciri miliyoyi a bankin Ethiopia

Published

on

Babban bankin kasuwancin Ethiopiya ya bai wa abokan hulɗarsa da suka ciri kuɗin da ya zarce wanda ke ajiye a asusunsu nan da ƙarshen makon nan su mayar da kuɗaɗen ko kuma su fuskanci shari’ah.

Kafafen yaɗa labarai a ƙasar sun ce fiye da dala miliyan 40 aka cira ko aka tura wasu bankuna a ranar Asabar da aka samu tangarɗa ta tsawon sa’oi a bankin na CBE.

A wata hira da BBC Newsday, shugaban bankin Abe Sano ya ce bankin ya gano akasarin hada-hadar da aka yi a lokacin da aka samu matsalar.

Da aka tambaye shi ko bankin zai kai rahoton waɗanda ba su mayar da kuɗin ba ga ƴansanda, Mista Abe ya ce “eh, eh sosai ma. Mun soma yin haka.”

Ya ƙara da cewa bankin zai ɗauki matakin shari’a kan waɗanda suka ƙi mayar da kuɗaɗen nan da ƙarshen makon nan”.

“Babu yadda za su tsira saboda abokan hulɗarmu ne. Mun san su. Za a iya gano su kuma za su yi bayanin abin da suka yi,” in ji Mista Abe.

Wasu kwastamomin da suka kwashi kuɗi mai yawan gaske tuni sun mayar wa bankin, in ji Mista Abe.

Sai dai ya ƙaryata rahotanni cewa kwastamominsu sun kwashi dala miliyan 40 inda ya ce kuɗin bai kai yawan wanda aka kwasa ba amma za a tantance yawansu bayan an gama gudanar da bincike nan gaba a makon nan.

Mista Sano ya ƙara da cewa ana yin bincike saboda wasu kwastamomi 10,000 da suka tura kuɗi lokacin da aka samu matsala sun yi haka ne kan ƙa’ida.

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara