Labarai
Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Kai Samame Gidan Kakakin Majalisar Afrika Ta Kudu
Masu bincike sun kai samame gidan shugabar majalisar dokokin kasar Afrika ta Kudu, bisa zargin da ake mata na cin hanci da rashawa, wanda hakan ya sanya ‘yan adawa suka bukaci ta yi murabus.
Hakan dai na zuwa ne watanni biyu kafin babban zaben kasar, a dai-dai lokacin da ake ci gaba da kai wa ‘ya’yan jam’iyar da ke mulki ta ANC samame, bisa zarginsu da aikata badakalar cin hanci da rashawa.
Hukumar da ke yaki da cin hancin da rashawa ta kasar dai ta tabbatar da cewa, wata babbar tawagar jami’anta sun kai samamen ne don gudanar da binciken a gidan shugabar majalisar Nosiviwe Mapisa-Nqakula da ke Johannesburg.
Majalisar dokokin kasar dai ta ce wannan binciken da ake yi wa Mapisa-Nqakula, na da alaka da zargin badakala da ake mata lokacin ta na ministar tsaron kasar.
Mapisa-Nqakula ta rike mukamin ministar tsoron kasar ne tsakanin shekarar 2014 zuwa 2021, kafin daga bisani aka nadata kakakin majalisar dokokin kasar, da hakan ya fuskanci suka daga bangaren ‘yan adawa.
-
Labarai7 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Tarakta 300 Ga Manoma Daga Amurka
-
Labarai20 hours ago
NAHCON Ta Jinjinawa Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Bisa Shirye-shiryen Hajjin Bana
-
Ilimi5 days ago
Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar Da Gidaje A Jami’ar Tarayya Da Ke Babura
-
Labarai20 hours ago
Amurka Ta Dakatar Da Kudurin Kai Jirgin Bama-Bamai Zuwa Isra’ila
-
Labarai5 days ago
An Samar Da Sabon Tsari Da Zai Inganta Harkar Noman Rogo A Najeriya
-
Fasaha2 days ago
Kusan Malaman Makaranta Dubu 2 Ke Samun Horo a Barno
-
Kasuwanci2 days ago
CBN Ya Bai Wa Masu POS Wa’adin Yin Rajista Da Gwamnati
-
Fasaha2 days ago
Bankuna Za Su Fara Cirar 0.5% Daga Masu Tura Kudi Ta Intanet