Connect with us

Fasaha

Gwamnatin Tarayya Za Ta gina babbar cibiyar lantarki mai amfani da rana a Najeriya

Published

on

Gwamnatin Tarayya ta sa hannu kan wata yarjejeniyar gina cibiyar samar da wutar lantarki mai amfani da ruwa da hasken rana da za ta samar da wuta mai ƙarfin megawatt 20.

Shirin samar da lantarki mai ƙarfin megawatt 300 wani ɓangare ne na ƙudurin Najeriya na komawa ga amfani da makamashi mara gurɓata muhalli.

Za a gina cibiyar a Shiroro da ke jihar Neja a tsakiyar Najeriya kuma zai zama shirin haɗin gwiwa tsakanin kamfanin NSP mai zaman kansa da hukumar NSIA mai bibiyar harkokin gwamnatin a Najeriya.

“Wannan wani shiri ne na farko na samar da lantarki mai amfani da hasken rana da ruwa,” in ji mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima lokacin rattaba hannu kan yarjejeniyar.

Ya ƙara da cewa shirin zai taimaka wa Najeriya ta faɗaɗa hanyoyin da take amfani da makamashi.

Najeriya dai na fama da matsalar rashin tsayayyiyar wutar lantarki tsawon shekaru duk da kasancewarta babbar mai samar da iskar gas da man fetur.

Lamarin yana yawan janyo matsala a babban layin da ke samar wa ƙasar wuta tare da jefa jama’a cikin duhu.

Galibin mutane a yanzu suna komawa amfani da injin janareto da wutar sola mai amfani da hasken rana domin kaucewa yawan dogaro ga babban layin wutar da ke yawan fuskantar matsala.

Labarai

Labarai16 hours ago

Gini Ya Fado Kan Mutane 11 A Kano

Wani gini ya fado kan ma’aikata suna tsaka da aikin gini a unguwar Kuntau da ke Karamar Hukumar Gwale a...

Ilimi18 hours ago

Gwamnatin Qatar Za Ta Tallafa Wa Marayu 1000 A Borno

Gwamnatin Kasar Qatar ta yi alkawarin tallafawa kimanin marayu dubu daya da rikicin Boko Haram ya rutsa da iyayensu. Jakadan...

Labarai3 days ago

Jihar Jigawa Za Ta Fara Allurar Rigakafi Da Bada Unifom Ga Alhazai

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce nan ba da dadewa ba za ta fara gudanar da allurar...

Ilimi3 days ago

Daliban Jihar Kebbi Da Ke Kasashen Waje Za Su Sami Tallafin Naira Miliyan 309

Gwamnatin jihar Kebbi, ta amince da kashe sama da Naira miliyan Dari Uku da Tara, domin biyan tallafin karatu na...

Kasuwanci3 days ago

Kwari Masu Lalata Amfanin Gona Sun Mamaye Gonakin Tumatur A Kano

Shugaban kungiyar manoma ta jihar Kano, AFAN, Abdullahi Maibreadi, ya bukaci gwamnati a dukkan matakai da su taimaka wa manoma...

Fasaha3 days ago

Shugaba Tinubu Ya Kaddamar Shirin Bada Bashin Kayyaki Ga ‘Yan Kasa

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya ƙaddamar da kashin farko na tsarin karɓar bashin kaya ga ƴan ƙasar. Bayanin hakan na...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Rufe Bankin UBA Kan Kin Biyan Haraji

Hukumar Tara Kudaden Haraji ta Jihar Kaduna (KADIRS) ta raufe rassan bankin UBA kan kin biyan harajin Naira miliyan 14....

Labarai4 days ago

Mutum Biyar Sun Mutu Cikin Kwale-Kwalen ƴan Ci-Rani

Mutum biyar har da yaro sun mutu yayin da suke ƙoƙarin tsallake hanyar ruwa da ta ratsa Ingila da safiyar...

Kasuwanci4 days ago

CBN Ya Sake Karya Farashin Dala Zuwa N1,101

Babban Bankin Nigeria CBN ya sake sanar da matakin karya farashin dala daga N1,251 zuwa N1,101. CBN ya bayyana haka...

Ilimi4 days ago

Ƴan Sanda Za Su Yi Bincike Kan Makarantar Leads British

Rundunar ƴan sanda a babban birnin tarayya Abuja ta ce ta aika tawagar jami’anta zuwa makarantar Leads British bayan bidiyon...

Mafi Shahara