Labarai
An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta samar da katafaren masauki kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah na kasar Saudiyya ga Alhazan jihar da za su sauke farali a bana.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga wakilin gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.
Ya ce hukumar ta samar da masauki mai daraja da zai yi gogayya da na sauran kasashen duniya kusa da masallacin Harami, domin baiwa Alhazan jihar damar zuwa masallacin ba tare da wata wahala ba.
Ya kuma bayyana cewa, Gwamna Umar Namadi ya kudiri aniyar bai wa hukumar duk wani tallafin da ya dace domin samun damar kulawa da Alhazan jihar yadda ya kamata.
Dangane da ciyarwa yayi aikin Hajji kuwa, Ahmed Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kulla yarjejeniya da wani kamfani don samar da ingantaccen abinci ga Alhazan jihar yayin gudanar da aikin Hajjin.
Ya ce, hukumar na da kwarin gwiwar cewa kamfanin zai cimma yarjejeniyar da suka kulla.
Shugaban ya yi nuni da cewa, za su rika bada kulawa ta musamman ga mahajjatan da ke fama da lalurar rashin lafiya don ganin su ma an samar musu abincin da ya dace da su.
Yayin da ya yaba wa ma’aikatan hukumar kan kwazon su, ya kuma umarce su da su sake sadaukar da kansu don ganin an samu nasarar aikin Hajjin bana.
Labbo ya bayyana godiya ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Umar Namadi da kuma hukumar Alhazai ta kasa NAHCON bisa goyon bayan da suke bai wa hukumar jin dadin alhazai ta jihar jigawa.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
