Connect with us

Labarai

An Samar Da Masauki Kusa Da Harami Ga Alhazan Jihar Jigawa

Published

on

Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa  ta samar da katafaren masauki  kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah na kasar Saudiyya ga Alhazan jihar da za su sauke farali a bana.

Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga wakilin gidan rediyon Najeriya a Dutse babban birnin jihar.

Ya ce hukumar ta samar da masauki mai daraja da zai yi gogayya da na sauran kasashen duniya kusa da masallacin Harami, domin baiwa Alhazan jihar damar zuwa masallacin ba tare da wata wahala ba.

Ya kuma bayyana cewa, Gwamna Umar Namadi  ya kudiri aniyar bai wa  hukumar duk wani tallafin da ya dace domin  samun damar kulawa da Alhazan jihar yadda ya kamata.

Dangane da ciyarwa yayi aikin Hajji kuwa, Ahmed Labbo ya bayyana cewa, hukumar ta kulla yarjejeniya da wani kamfani don samar da ingantaccen abinci ga  Alhazan jihar  yayin gudanar da aikin Hajjin.

Ya ce, hukumar na da kwarin gwiwar cewa kamfanin zai cimma yarjejeniyar da suka kulla.

Shugaban ya yi nuni da cewa, za su rika bada kulawa ta musamman ga mahajjatan da ke fama da lalurar rashin lafiya don ganin su ma an samar musu abincin da ya dace da su.

Yayin da ya yaba wa ma’aikatan hukumar kan kwazon su, ya kuma  umarce su da su sake sadaukar da kansu don ganin an samu nasarar aikin Hajjin bana.

Labbo ya bayyana godiya ga gwamnatin jihar karkashin jagorancin gwamna Umar Namadi da kuma hukumar Alhazai ta kasa NAHCON bisa goyon bayan  da suke  bai wa hukumar jin dadin alhazai ta jihar jigawa.

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara