Connect with us

Labarai

An Kashe Jagoran ‘Yan Adawar Chadi Yaya Dillo

Published

on

Hukumomin kasar Chadi sun tabbatar da mutuwar daya daga cikin shugaban ‘yan adawa Yaya Dillo bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai ofishin jam’iyyarsa a jiya, wanda ya jefa mazauna birnin Ndjamena cikin fargaba da tashin hankali.

Mai gabatar da kara na gwamnatin Chadi Oumar Mahamat Kedelaye ya tabbatar da mutuwar shugaban ‘yan adawar a yau Alhamis, bayan artabun da akayi jiya.

Mutuwar Dillo na zuwa ne bayan da gwamnatin kasar ta zargi jam’iyyarsa da kai wani mummunan hari kan hukumar tsaron kasar, lamarin da ya musanta shi kai tsaye a jiya Laraba.

Harin da aka kai kan hukumar tsaron ya zo ne bayan da aka kama wani ‘dan jam’iyyarsa ta PSF tare da zargin sa da yunkurin kisan shugaban kotun kolin kasar.

A jiya Laraba ne aka ji karar harbe-harbe a kusa da hedikwatar jam’iyyarsa da ke N’Djamena babban birnin kasar.

 

Wannan na zuwa ne kwana guda da gwamnatin Chadi ta sanar cewa, za a gudanar da zaben shugaban kasa a ranar 6 ga watan Mayu, inda shugaba Mahamat da Dillo za su fafata da juna.

Mahamat dai ya dare kan karagar mulki ne bayan mutuwar mahaifinsa Idriss Deby Itno wanda ya rasa ransa a yayin fafatawa da ‘yan tawaye a 2021, yayin da ya shafe kimanin shekaru 30 yana mulkar kasar kafin ajalinsa.

 

Har ya zuwa wannan lokaci mazauna babban birnin kasar na cikin fargaba dangane da abin da ka iya je ya komo, sakamakon arangamar ta jiya da kuma mutuwar shugaban ‘yan adawa

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara