Connect with us

Labarai

An Bukaci Kiristocin Kwara Su Taimaki Wasu a Sabuwar Shekara

Published

on

An yi kira ga Kiristoci a jihar Kwara da su yi amfani da ni’imomin da Allah Ya hore musu wajen inganta rayuwar sauran al’umma, musamman masu bukata, a wannan sabuwar shekara.

Bishop na Cocin Anglican, Right Reverend Sunday Adewole, ne ya yi wannan kira a cikin sakon sabuwar shekararsa da ya gabatar wa mabiya a cocin St. Barnabas Cathedral da ke Ilorin.

Ya ce akwai matuƙar buƙatar masu hali su tallafa wa marasa galihu domin faranta musu rai da rage musu wahalhalu.

A cewarsa, idan lokaci ya yi na zuwa wurin aiki, bai dace mutum ya kasance yana coci yana ibada ba, domin kowane abu yana da lokacinsa.

Bishop Adewole ya jaddada cewa lokaci ya yi da ya kamata kowa ya ɗauki aikinsa da muhimmanci sosai, tare da guje wa sakaci da lalaci a harkokin kasuwanci ko aiki.

Ya ƙara da cewa ya dace a ba kowane abu muhimmancin da ya dace da shi, yana mai cewa duk wanda ke neman wadata da ci gaba, ya nemi taimakon Allah ta hanyar roƙon Ubangiji.

Bishop Adewole ya kuma shawarci mabiya da su nuna ƙauna da himma a aikinsu, su saita manufofi domin tabbatar da ci gaba da bunƙasa rayuwa a wannan sabuwar shekara.

Limamin ya ƙara da kiran da ya yi musu na ci gaba da kasancewa masu yawan addu’a, tare da sadaukar da kansu ga karatun Littafi Mai Tsarki a kowane lokaci, domin samun nasara a rayuwarsu.

Haka kuma ya gargade su da su kasance masu gamsuwa da abin da suke da shi, tare da ladabi da bin doka, domin hakan ne zai taimaka musu wajen cimma burinsu a rayuwa

Ali Muhammad Rabiu

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara