Labarai
An Bai Wa Alhazan Jihar Naija Tabbacin Samun Kyakkyawar Kulawa Yayin Aikin Hajji
Alhazan jihar Neja sun samu tabbacin kyautata walwala da jin dadinsu yayin da suke kasa mai tsarki don gudanar da aikin hajjin bana.
Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Yakubu Garba ya ba da wannan tabbacin ga jirgin karshe na jigilar alhazan jihar daga filin jirgin sama na Bola Ahmad Tinubu da ke Minna zuwa birnin Madina na kasar Saudiyya.
Kwamared Yakubu Garba ya ce gwamnatin jihar Naija a karkashin jagorancin Gwamna Mohammed Umar Bago Alhazan jihar ta yi tanadi na musamman ga Alhazan domin samun kyakkyawar kulawar da ta da ce yayin gudanar da aikin hajjin bana ba tare da wata matsala ba.
Ya kuma yi kira ga Mahajjatan da su yi addu’a ga jihar Neja da kasa baki daya, domin fatan Allah Ya warware dukkan kalubalen da ake fuskanta.
A nasa jawabin Amirul Hajj na jihar kuma Sarkin Kagara, Ahmed Garba Gunna Attahiru na biyu, ya bayyana jin dadinsa bisa goyon baya da hadin kan da Gwamna Umar Bago ya ba su domin gudanar da aikinsu.
Ya ce a nasu bangaren mambobin tawagarsa za su yi duk mai yiwuwa don tabbatar da ganin sun sauke nauyin da aka daura musu.
Aliyu Lawal
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
