Connect with us

Labarai

Ambaliyar Ruwa ta Shafe Manyan Titunan Birnin Dubai

Published

on

 

Ambaliyar ruwa ta rufe manyan titunan birnin Dubai kuma babban filin jirgin samansa ya kasance cikin rudu yayin da cibiyar hada-hadar kudi ta Gabas ta Tsakiya din ta kasance a kulle a ranar Laraba, kwana guda bayan da aka yi ruwan sama mai tsananin gaske da ba a taba irinsa ba.

A kalla mutum daya ya mutu, wani dattijo mai shekaru 70 da haifuwa, a cikin motarsa a Ras Al-Khaimah, daya daga cikin masarautun kasar bakwai masu arzikin man fetur, in ji ‘yan sanda.

An samu katsewar wutar lantarki a kusa da birnin Dubai, wanda ke cike da ambaliyar ruwa da ya nitsar da motocin da aka bari.

An ga irin wannan al’amuran a kusa da yankunan da suka hada da Sharjah, makwabciyar Dubai, inda mazauna yankin suka yi ta ratsa manyan tituna tare da kai komo a cikin kwale-kwale na wucin gadi.

“Wannan shi ne lamari mafi muni da na taba fuskanta,” in ji wani dan kasar Dubai mai shekaru 30, wanda ya so a sakaya sunansa, bayan wata tafiyar tsawon mintuna 15, ya koma sa’o’i 12 a kan tituna da ambaliyar ruwa ta mamaye.”

“Na san cewa idan motata ta lalace zata nutse ni ma kuma zan nutse da ita.”

Makarantu za su ci gaba da kasancewa a rufe a Dubai har zuwa mako mai zuwa, in ji hukumomi, wanda ke nuna irin wahalar tsaftace muhallin.

A halin da ake ciki, ayyuka suna yi tafiyar hawainiya a filin jirgin sama na Dubai, mai tasha mafi yawan zirga-zirgar jiragen sama a duniya, yayin da ma’aikatan suka kasa isowa aiki sakamakon ambaliyar ruwa, sannan kuma aka dakatar da akasarin motocin zirga-zirgar jama’a.

Yayin da aka jinkirta kusan kowane jirgi akai-akai, an gaya wa fasinjoji su nisanci filin “sai dai idan ya zama dole,” in ji ma’aikatan Filin jirgin saman Dubai.

An kuma jinkirta tashin jirage da dama, an soke da kuma karkatar da su a lokacin da aka yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a ranar Talata, lokacin da jiragen suka ce su na yunkurin tashi cikin ruwa mai zurfi.

Guguwar ta afka wa kasashen Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain ne da daren jiya litinin da kuma ranar Talata bayan da a baya suka afka wa kasar Oman, inda mutane 19 suka mutu ciki har da kananan yara.

Maryam Al Shehhi, babbar jami’ar hasashen yanayi a cibiyar nazarin yanayi ta UAE, ta musanta rahoton da ke cewa Hadaddiyar Daular Larabawa ta yi shukar gajimare inda ta fesa sinadarai don kara yawan ruwan sama.

VOA

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara